Rundunar sojin Amurka ta ce ta kai hari kan wasu jiragen dakon mai guda uku na Iran a ranar Asabar, bayan da aka harba makamai masu linzami kan jiragen ruwan yaƙin Amurka.

Rundunar ta kuma yi gargadin cewa za ta iya “lalata jiragen dakon man Iran idan hakan ya zama dole.

A cikin wata sanarwa, rundunar sojin Amurka ta ce wani jirgin ruwan yaƙi mai ɗauke da jiragen sama da kuma wani jirgin ruwan yaƙi mai linzami sun tsallake hare-haren da Iran ta kai musu ba tare da wani dalili ba, yayin da suke sintiri a yankin.

Ta ce babu wani jami’in Amurka da ya ji rauni.

Rundunar ta ce an lalata gaba ɗayan wasu jiragen dakon mai guda biyu na Iran, yayin da jirgin na uku, wanda babu kaya a cikinsa, shi ma aka lalata.

Amurka ta bayyana cewa jiragen dakon man suna cikin wata hanya ta ɓoye da ake amfani da ita wajen samar da kuɗaɗen tallafawa Rundunar Juyin Juya Hali ta Iran da kuma ƙungiyoyin da take ɗaukar nauyinsu da makamai a yankin.

Hare-haren sun zo ne kusan mako guda bayan Amurka da Iran sun sake komawa kai hare-hare, bayan shafe kusan wata guda cikin kwanciyar hankali. Rikicin da ke faruwa lokaci-lokaci ya fara ne a ranar 28 ga Fabrairu, bayan hare-haren da Amurka da Isra’ila suka kai.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *