[Hoto: Yeni Şafak]

Gwamnatin Jamus ta fito fili ta zargi Rasha da hannu a wani yunkurin harin ta’addanci da aka shirya, ta hanyar amfani da jirgi marar matuki makare da bama-bamai a kan wani babban filin jirgin sama a gabashin kasar.

Ministan Cikin Gida na Jamus, Alexander Dobrindt, ya ce Rasha ce ta kitsa yunkurin harin akan  filin jirgin saman Leipzig/Halle a ranar 4 ga watan Agusta, wanda a sakamakon haka Berlin ta dauki matakin rufe ofishin jakadancin Rashan dake Bonn kafin 18 ga watan Satumba.

[Hoto: Constantin von Hoffmeister]
Haka nan Jamus ta soke kwangilar tsara gidan al’adun Rasha da ke birnin Berlin, bayan kammala binciken tare da tabbatar da cewa Rasha ce ke da hakkin kitsa harin na sirri da aka shirya kaiwa Leipzig, in ji Minista Dobrindt.

[Hoto: Iren in Russia]
A yammacin ranar 4 ga watan Agusta ne aka tsinci jirgin dauke da giram 800 na ababen fashewa, a kusa da wani jirgin saman dakon kaya na kasar Ukraine kirar (Antonov), da ke aiki a karkashin shirin NATO.

Kasashe da dama a nahiyar Turai da ke bai wa Ukraine goyon baya suna fuskantar karuwar laifukan da suka shafi zagon kasa tun bayan fara yakin Ukraine.

[Hoto:Kyiv Post]

Yayin da Kungiyar Tarayyar Turai (EU) da Kungiyar Tsaro ta NATO suka yi alkawarin ba da cikakken goyon baya, an gano cewa filin jirgin saman na Leipzig shi ne babbar cibiyar sarrafa kayan agaji da makamai zuwa Ukraine.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *