Brentford ta samu gagarumar nasara a kan Chelsea, bayan ta doke ta da ci 3-0 a wasan mako na biyar na gasar Premier League da suka fafata a filin wasa na  Gtech Community.

Damsgaard ne ya taka muhimmiyar rawa wajen nasarar Brentford, inda ya taimaka wajen samar da damar ƙwallayen farko da na biyu. Yarmoliuk ne ya fara tabawa kwallon kai kafin Anthony ya zura ta a raga, sannan Thiago ya kara ta biyu bayan an kubutar da kwallon farko da mai tsaron ragar Chelsea ya yi.

A mintunan ƙarshe ne Fabio Carvalho ya kammala nasarar Brentford da ƙwallo ta uku, bayan da Schade ya taka muhimmiyar rawa wajen kai harin.

Wannan nasara ta sa Brentford ta ci gaba da nasara a wasanni biyar na farko na kakar bana, yayin da Chelsea ta fuskanci babban rashin nasara a karkashin sabon kocinta, Xabi Alonso.

Chelsea kuma ta zama ƙungiyar da Brentford ta fara doke wa a gida tun bayan komawarta gasar Premier League, yayin da Brentford ta zama ƙungiyar farko da ta hana Chelsea zura ƙwallo a wannan kakar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *