Iran ta ce a ranar Lahadi dakarunta sun kai hari kan wani jirgin ruwa mara matuki na sojojin Amurka da ke ƙoƙarin shiga mashigar Hormuz, sa’o’i kaɗan bayan da ta kai hari kan wasu jiragen ruwa a matsayin ramuwar gayya kan hare-haren da Amurka ta kai kan jiragen dakon man fetur guda uku.
Sabon zagayen arangamar, wanda ya fara ne bayan hare-haren da Amurka ta kai a makon da ya gabata, ya faru ne a daidai lokacin da aka samu tsaiko a yaƙin da ke tsakanin ƙasashen biyu, wanda yanzu ya shafe watanni shida.
- Aƙalla Mutane 25 sun mutu a hatsarin bas a Cape Verde
- Amurka ta kai hari kan jiragen dakon mai uku na Iran
- Rikici a Mashigar Hormuz ya ƙara farashin mai yayin da Amurka da Iran ke ikirarin sarrafa hanyar ruwa
Iran ta ci gaba da ƙarfafa iko da mashigar Hormuz mai matuƙar muhimmanci, yayin da Amurka ke ci gaba da aiwatar da wani shirin toshe hanyoyin jiragen ruwa zuwa tashoshin jiragen ruwa na Iran.
Washington na kuma ƙoƙarin durƙusar da tattalin arzikin Iran ta hanyar kakaba takunkumi kan ƙungiyoyi da hukumomin da ke da alaƙar kuɗi da Jamhuriyar Musulunci ta Iran, da nufin tilasta mata yin biyayya.
Babban mai shiga tattaunawar Iran, Mohammad Bagher Ghalibaf, ya yi barazanar cewa Iran za ta ƙaddamar da martani cikin sauri da kuma mafi ƙarfi kan hare-haren Amurka.