Kimanin mutane 49 sun rasu a cikin hamadar Sahara dake iyakar Nijar da Mali da Aljeriya dake da tazarar km 80 a yammacin Asamaka
Wata sanarwa daga ofishin Gwamnan jihar Agadez Janar Ibra Boulama, tace matafiyan nacikin wata babbar motar da ke dauke da mutanen da aka kiyasta cewa sun haura 40
- Kotu a Yamai ta bayar da belin Gazali Abdou Tasaoua
- An bude Sabuwar Tashar Lantarki a Birnin Yamai
- Trump ya kammala ziyararsa a China: Amma me zai biyo baya?
A cewar wasu shaidu motar ta taso ne daga kauyen Telhandek da ke da tazarar km 300 da iyakar Nijar dauke da wasu ‘yan kasar a kan hanyarsu ta zuwa gida domin shagulgulan sallar layya kafin direban ya yi batan Kai a hamada, lamarin da ya haddasa karancin ruwan sha da yayi ajalin mutanen
A kalla mutane 49 ne aka yi jana’izar su a wurin da abin ya faru a cewar ofishin Gwamnan Agadez yayin da wasu mutane 2 daga cikin fasinjojj suka tsira da ransu
