Sai dai Shugaban Mulkin Sojan Kasar Janar Abdourahamane Tiani ya tashi zuwa Birnin Ankara domin ziyarar aiki ta kwanaki Uku, bisa gayyatar da shugaban Turkiyya Recep Tayyip Erdogan yayi masa.
A bayan Bayan nan dai alamu na nuna yadda kasar ke samun gagarumin sauyi ta fuskar kyautata alaka da kasashen waje.
Ko a ranar Talata 2 ga watan Yuni Sabon Shugaban Jamhuriyar Benin Romuald Wadagni ya kai ziyarar sabunta alaka Yamai, bayan da Nijar ta kulle kan iyakar ta shekaru Uku da suka gabata.
Gwamnatin Mulkin Soja a Jamhuriyar Nijar ta zargi tsohuwar Gwamnatin Shugaba Patrice Talon da marawa Faransa baya domin hambarar da gwamnatin Janar Abdurrahmane Tiani.
