Rebecca Adegbemile, yayin murnar shan kwallo da ta yi

Tawagar Falconets ta Najeriya ta lallasa ƙasar New Caledonia da ci 10-1 a wasan ƙarshe na rukunin F na Gasar Cin Kofin Duniya na Mata ‘yan ƙasa da shekaru 20 da suka buga a ranar Lahadi, a ƙasar Poland.

Falconets ta samu damar tsallakawa zuwa zagaye na 16 bayan ta haɗa maki 4 daga wasanni uku da ta buga.

Ramotalahi Kareem da Onajite David, kowannen su, ta ci kwllo uku-uku, sannan kuma Rebecca Adegbemile ta ci ƙwallo biyu, sai kuma Janet Akekoromowei ta ci ƙwallo ɗaya, da kuma Tosin Rafiu ƙwallo ɗaya.

‘Yar wasa Joceline Kourevi ce ta ci wa New Caledonia ƙwallo ɗayan da ta ci a minti na 89.

Spaniya ce ke matsayi na farko a rukunin na F bayan ta doke China da ci 3-1.

Spaniya, da Najeriya, da kuma China duk sun tsallaka zuwa matakin zagaye na 16, yayin da New Caledonia ta fice bayan ta sha kashi a wasanni uku a jere.

Falconets ta sha wahala a farkon wasan, inda ta fara da yin rashin nasara da ci 2-0 a hannun Spaniya a wasanta na farko, sannan kuma ta tashi 0-0 da China.

Yanzu Najeriya tana jiran a kammala wasannin rukuni na E domin sanin wadda za ta zama abokiyar fafatawarta a zagaye na 16 da kuma sanin jadawalin wasan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *