Bayan wasannin farko da suka zo da sakamako masu ban mamaki, musamman nasarar Hull City kan Manchester United da kuma Brighton da ta lallasa Aston Villa, za a dawo mako na 2 a gasar ta Premier League, inda kowace ƙungiya ke neman gina kwarin gwiwa ko kuma ta farfaɗo daga rashin nasara.

A daren Juma’a, Crystal Palace za ta karɓi Manchester City a Selhurst Park. Palace ta fara kakar bana da rashin nasara a hannun Everton da ci 2–0, yayin da Manchester City ta fara sabon zamaninta ƙarƙashin Enzo Maresca da nasara ta 2–1 a kan Bournemouth.

City ce ke da rinjaye a tarihin karawar kungiyoyin biyu, inda a cikin wasannin Premier League 26 da suka gabata ta samu nasara 18, Palace ta yi nasara uku, yayin da aka tashi kunnen doki sau biyar.

A cikin karawarsu ta baya-bayan nan ma City ta doke Palace 3–0 a Etihad. Wannan ya sa City za ta shiga wasan da ƙarin kwarin gwiwa, amma Palace na da damar yin amfani da kasancewar ta gida wajen neman maki na farko bayan fara kakar.

Hoto: Google

A ranar Asabar, Liverpool za ta karɓi baƙoncin Nottingham Forest a Anfield. Liverpool ta fara kakar da canjaras 2–2 da Newcastle, inda Cody Gakpo da Dominik Szoboszlai suka zura ƙwallayen da suka dawo da ita wasan. Forest kuwa ta sha kashi a hannun Leeds da ci 1–0, sannan Leeds ta sake doke ta a Carabao Cup.

Wannan wasa zai zama gwaji ga sabon kocin Liverpool, Andoni Iraola, musamman wajen gyara matsalolin tsaro da rashin daidaiton tsakiyar fili.

Tarihin baya-bayan nan ma ya sa wasan ya fi ɗaukar hankali, domin Forest ta lashe wasannin lig biyu na ƙarshe da Liverpool a Anfield, amma Liverpool ba ta taɓa yin rashin nasara a wasannin farko na kakar wasa a Anfield ba tun 2003.

Hoto: Google

Bournemouth za ta karɓi Everton a filin wasa Vitality. Bournemouth ta fara kakar da rashin nasara 2–1 a hannun Manchester City, duk da cewa ta taka rawar gani na wani lokaci, yayin da Everton ta samu nasara 2–0 a kan Crystal Palace. Don haka Everton za ta shiga wasan cikin yanayi mai kyau, amma Bournemouth na da damar gyara sakamakonta a gaban magoya bayanta.

Tarihin karawarsu ya yi kusa sosai: sun haɗu sau 24 a dukkan gasa, Bournemouth ta yi nasara 11, Everton ma 11, yayin da aka tashi kunnen doki sau biyu.

Hoto: Google

Coventry City kuma za ta karɓi baƙoncin Hull City a wani wasa da ake iya kallonsa a matsayin farkon gwajin kungiyoyin da suka samu gurbin Premier League. Coventry ta sha kashi 3–0 a hannun zakarun gasar Arsenal a makon farko, yayin da Hull ta yi abin mamaki ta doke Manchester United 2–0. Saboda haka Hull za ta shiga wasan da ƙwarin gwiwa, yayin da Coventry ke neman samun maki na farko.

Wannan shi ne wasan farko da Coventry za ta buga a gida a Premier League bayan shafe shekaru 25.

Tarihin karawar kungiyoyin biyu ya samo asali ne tun kafin zamanin Premier League, kuma wannan fafatawar na da muhimmanci saboda dukkansu za su ɗauke ta a matsayin damar tara maki daga ƙungiyar da ke fafutukar matsayi iri ɗaya.

Hoto: Google

A filin wasa na Tottenham Hotspur, Tottenham za ta karɓi bakoncin Newcastle United. Spurs ta fara kakar da mummunar rashin nasara 3–0 a hannun Brentford, amma ta farfaɗo a tsakiyar mako da nasarar 5–1 a kan Charlton a Carabao Cup. Newcastle kuwa ta yi canjaras 2–2 da Liverpool, sannan ta doke West Brom 3–2 a gasar League Cup.

Tarihin baya-bayan nan ya karkata zuwa Newcastle, wadda ta doke Tottenham 2–1 a Tottenham Hotspur a watan Fabrairu, sannan ta kuma yi nasara a wasanni biyu na baya-bayan nan da ta ziyarci filin Spurs. A gaba ɗaya, kungiyoyin biyu sun yi karawa da yawa, inda Tottenham ke da nasarori 74 a dukkan gasa, Newcastle 66, tare da kunnen doki 35.

Hoto: Google

A ranar Lahadi, Chelsea za ta karɓi bakoncin Brighton a Stamford Bridge. Chelsea ta fara kakar da nasara 3–2 a kan Fulham, inda Cole Palmer ya taka muhimmiyar rawa, yayin da Brighton ta aika babbar sanarwa tun farkon kakar bayan ta doke Aston Villa da ci 4–0. Wannan zai zama babban gwaji ga sabon kocin Chelsea, Xabi Alonso, saboda Brighton ta samu nasara a kan Chelsea a wasanni biyu na Premier League da suka gabata, ciki har da 3–0 da ta yi a Brighton a watan Afrilu da 3–1 a Stamford Bridge a Satumba 2025. Duk da haka, a tarihin Premier League gaba ɗaya Chelsea ce ke da rinjaye, da nasarori 13 zuwa biyar na Brighton, yayin da aka yi kunnen doki sau huɗu.

Hoto: Google

Leeds United za ta karɓi bakoncin Brentford a Elland Road. Leeds ta fara kakar da nasara 1–0 a kan Nottingham Forest, sannan ta sake doke Forest a Carabao Cup, yayin da Brentford ta fara gasar da gagarumar nasara 3–0 a kan Tottenham. Wannan zai kasance wasa tsakanin kungiyoyi biyu da suka fara kakar cikin ƙwarin gwiwa. A tarihin karawarsu a Elland Road kuwa, Brentford ba ta samu nasara a kan Leeds tun shekarar 2015 ba, yayin da wasanni uku na Premier League da suka gabata tsakanin kungiyoyin biyu suka ƙare da kunnen doki. Hakan na nuna cewa wasa na iya kasancewa mai tsauri kuma mai ƙarancin tazara.

Hoto: Google

Sunderland za ta karɓi Fulham a filin wasa na Stadium of Light. Sunderland ta dawo Premier League da rashin nasara 2–1 a hannun Ipswich, yayin da Fulham ta sha kashi 3–2 a hannun Chelsea a Craven Cottage. Don haka kungiyoyin biyu na neman sakamakon da zai dawo musu da kwarin gwiwa. Tarihin karawarsu na baya-bayan nan ya karkata zuwa Fulham, wadda ta doke Sunderland 1–0 a watan Nuwamba 2025 sannan ta sake doke ta 3–1 a filin wasa na Stadium of Light a Fabrairu 2026. A Premier League ma Fulham ta fi Sunderland rinjaye a karawarsu, inda ta samu nasara 10 daga cikin 22, Sunderland biyar, aka yi kunnen doki bakwai.

Hoto: Google

A Old Trafford, Manchester United za ta karɓi Ipswich Town. Wannan wasa ne da ke ɗauke da matsin lamba musamman ga United, bayan da Hull City ta girgiza ta da ci 2–0 a makon farko. Ipswich kuwa ta dawo Premier League da nasara 2–1 a kan Sunderland, sannan ta ci gaba da samun nasara a Carabao Cup. Michael Carrick na bukatar amsa daga ‘yan wasansa, amma Carlos Baleba, sabon ɗan wasan United da aka ɗauko daga Brighton, ba zai buga wasan ba saboda raunin idon sawunsa. A tarihin karawarsu, United na da babban rinjaye a Old Trafford: ba ta yi rashin nasara a wasannin lig takwas na gida da Ipswich ba, inda ta yi nasara shida da kunnen doki biyu. Haka kuma Ipswich ba ta doke United a Premier League ba cikin wasanni bakwai da suka gabata ba.

Hoto: Google

Za a kammala wasan mako na 2 ranar Litinin da babban wasa tsakanin Aston Villa da Arsenal a Villa Park. Villa ta fara kakar bana da abin kunya, bayan Brighton ta lallasa ta 4–0, yayin da Arsenal ta nuna ƙarfinta da doke Coventry 3–0. Arsenal za ta shiga wasan cikin kyakkyawan yanayi, amma Villa na da tarihin iya jefa mata matsala. A bara, Villa ta doke Arsenal 2–1 a filin wasa na Villa Park, kafin Arsenal ta rama da nasarar 4–1 a Emirates. Gaba ɗaya kuma Arsenal ce ke da rinjaye a tarihin karawarsu, da nasarori 82 zuwa 67 na Villa, tare da kunnen doki 40. Sai dai Villa ta samu nasarori uku a cikin wasanni biyar na baya-bayan nan da Arsenal, abin da ke nuna cewa wannan ba wasa ne da zakarun za su ɗauka da wasa ba.

Hoto: Google

Gaba ɗaya, wasan mako na 2 na ɗauke da tambayoyi masu yawa. Shin Manchester United za ta iya farfaɗowa? Shin Liverpool za ta samu nasarar farko a ƙarƙashin Iraola? Shin Brighton za ta ci gaba da abin da ta fara a kan Chelsea? Kuma shin Arsenal za ta ci gaba da nuna cewa ita ce ƙungiyar da za yi bajinta a wannan kakar?

Wannan shi ne abin da za a kalla a mako na biyu na Premier League.

 

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *