Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana cewa an kama wasu kwamandojin ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP guda bakwai a Filin Jirgin Sama na Katsina yayin da suke dawowa daga aikin Hajji a ƙasar Saudiyya.

Ya ce an samu nasarar kamen ne sakamakon haɗa bayanan Hukumar Bayar da Lambar Shaidar Dan Ƙasa (NIMC) da na Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya da kuma tsarin bayanan hukumomin tsaro na ƙasa da ƙasa.

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a bayan Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rattaba hannu kan Dokar Hukumar Bayar da Lambar Shaidar Ƙasa (NIMC) ta shekarar 2026.

Gwamnatin Tarayya ta ce sabuwar dokar za ta ƙarfafa tsarin tantance bayanan ‘yan ƙasa, inganta tsaron ƙasa, sauƙaƙa samar da ayyukan gwamnati da kuma hanzarta sauyin fasahar zamani.

A cewar Tunji-Ojo, sabuwar dokar za ta ƙara inganta haɗin gwiwa tsakanin hukumomi, ta ƙarfafa sahihancin tsarin Lambar Shaidar Ƙasa (NIN), tare da taimakawa wajen yaƙi da ta’addanci, satar bayanan jama’a, laifukan kuɗi da sauran barazanar tsaro.

Ya ce haɗa bayanan NIMC da sauran bayanan gwamnati ya riga ya fara haifar da sakamako mai kyau, inda ya bayyana cewa kwamandojin Boko Haram da ISWAP bakwai da aka kama a makon da ya gabata an miƙa su ga Hukumar Tsaron Farin Kaya ta DSS domin ci gaba da bincike.

Ministan ya ƙara da cewa kafin aiwatar da waɗannan sauye-sauye, hukumomin gwamnati na gudanar da tsarin tantance bayanai daban-daban ba tare da haɗin kai ba. Ya ce a halin yanzu ba za a iya samun fasfo na Nijeriya ba sai an tabbatar da bayanan mutum ta hanyar tsarin NIMC, matakin da ya ce zai taimaka wajen ƙarfafa tsaro da inganta sahihancin bayanan ‘yan ƙasa.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *