Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta kama wani mutum da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai tare da kwato harsasai, mujallar bindigar AK-47, kayan soji da kuma wasu kayayyaki a ƙaramar hukumar Bichi.                                                                                                   

A cikin wata sanarwa, rundunar ta ce jami’anta sun kai samame ne bayan samun sahihan bayanai daga wani da ya sanar da su cewa an ga wani mutum sanye da kayan soji a ƙauyen Rimawa.

Ta ce tare da haɗin gwiwar al’ummar Rimawa, sun kama Mohammed Isah Haruna mai shekara 28, ɗan unguwar Dan Dinshe Yamma da ke ƙaramar hukumar Dala.

‘Yan sandan sun ce sun gano bindigar AK-47 ɗauke da harsasai 30 da ƙarin harsasai 79 da kayan soji guda biyu da hulunan soji uku da katin shaidar soja da ake zargin na bogi ne, da kuma wasu katunan shaida, katunan ATM huɗu da takalman soji.

Rundunar ta ce wanda ake zargin ya amsa cewa ya kai kayan ne domin miƙa su ga ‘yan bindigar da ke buya a daji.

Kwamishinan ‘yan sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya yaba wa al’ummar Rimawa bisa bayar da bayanan da suka taimaka wajen kama wanda ake zargin.

Ya ce bincike ya fara domin gano sauran waɗanda ake zargi da hannu a lamarin, kuma za a gurfanar da wanda aka kama a kotu bayan kammala bincike.

Rundunar ta kuma buƙaci jama’a su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanan sirri domin inganta tsaro.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *