Hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa NDLEA ta ayyana wani da ake zargi da jagorantar ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi, Nnamuka Kelvin Uchenna, wanda aka fi sani da Odogwu, tare da wasu mutum uku, a matsayin waɗanda hukumar ke nema ruwa a jallo.
A cewar NDLEA, kotun tarayya da ke Owerri a jihar Imo ce ta ba da umarnin ayyana mutanen bayan bincike ya danganta su da wata ɓoyayyar cibiyar da ake kera sinadarin methamphetamine a ƙaramar hukumar Njaba ta jihar Imo.
- Akalla mutum 20 sun mutu a hare-haren ‘yan ta’adda a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo (DRC)
- Yara 20 sun mutu a hatsarin motar bas a Uganda
Hukumar ta ce jami’anta sun gano cibiyar ne a watan Fabrairun 2026, inda suka ƙwace kilo 18.4 na sinadarin methamphetamine tare da wasu kayayyakin da ake amfani da su wajen sarrafa miyagun ƙwayoyi.
NDLEA ta ce binciken kimiyya ya gano cewa waɗanda ake nema sun tsere, yayin da ake ci gaba da farautarsu domin gurfanar da su a gaban kotu.