Hukumar NDLEA ta sanar da cewa ta samu nasarar rufe asusun banki da ke ɗauke da sama da Naira biliyan 9.8, waɗanda ake alaƙantawa da wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi.

Hukumar ta ce ta kuma samu umarnin kotu na wucin gadi na ƙwace wasu kadarori masu darajar biliyoyin naira, ciki har da gidan mai da manyan gine-gine da kuma motocin alfarma guda huɗu.

NDLEA ta bayyana cewa matakin ya biyo bayan binciken kuɗaɗen da ake zargin an samu daga harkokin miyagun ƙwayoyi, domin dakile hanyoyin da ƙungiyoyin masu aikata laifuka ke amfani da su wajen ɓoye dukiyoyinsu.

Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa mai ritaya, ya ce hukumar za ta ci gaba da bibiyar manyan masu safarar miyagun ƙwayoyi da kuma kadarorin da suka mallaka ta hanyar haramtacciyar hanya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *