Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Sakkwato ta ce ta ƙwato dabbobi 689 da ‘yan bindiga suka sace a sassa daban-daban na jihar, sakamakon hare-haren da jami’anta suka dakile tsakanin watan Mayu zuwa yanzu.

Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Hayatu Hassan Shaffa ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da ya gudanar a Sakkwato, inda ya ce an gudanar da samamen ne a ƙananan hukumomin Tangaza da Wamakko da Tureta da Bodinga.

Ya ce jami’an rundunar sun yi artabu da ‘yan bindigar a lokuta daban-daban, inda suka ƙwato dabbobin tare da kama wasu daga cikin waɗanda ake zargi.

Shaffa ya ƙara da cewa an mayar da dabbobin da aka ƙwato ga masu su, yana mai jaddada cewa rundunar za ta ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *