Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ce tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), da sauran waɗanda suka yi iƙirarin mallakar wasu kadarori 48 sun kasa gabatar da hujjojin da ke nuna cewa sun mallake su ne ta hanyar halastacciyar hanyar samun kuɗi.
Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta bayyana hakan ne yayin da take yanke hukuncin ƙwace kadarorin tare da mayar da su hannun Gwamnatin Tarayya.
Kotun ta ce Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta gabatar da hujjojin da suka isa su nuna cewa ana zargin kadarorin sun samo asali ne daga haramtattun ayyuka, yayin da waɗanda ake ƙara suka gaza sauke nauyin da doka ta ɗora musu na bayyana sahihin asalin kuɗin da aka yi amfani da su wajen sayen kadarorin.
- ‘Yan sanda a Kano sun kama wanda ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai a Bichi
- Sarkin Musulmi Ya Ayyana Ranar Farko Ta Watan Safar 1448 bayan Hijira
Mai shari’ar ta ƙara da cewa a irin wannan shari’ar ƙwace kadara, ba wai kawai mutum ya ce kadarar tasa ba ne ya isa, sai ya nuna hujjojin yadda ya mallake ta ta hanyar doka.
Hukuncin ya shafi kadarori 48 da suka haɗa da Jami’ar Rayhaan da Rayhaan Radio da otal-otal da gidaje da filaye da masana’antu da wasu kadarori da ke jihohin Kebbi da Kano da Babban Birnin Tarayya.
EFCC ta bayyana hukuncin a matsayin wata babbar nasara a yaƙin da take yi da cin hanci da rashawa da kuma ƙwato kadarorin da ake zargin an mallake su ba bisa ƙa’ida ba.