Tawagar 'yan wasan Flying Eagles yayin atisaye.

Flying Eagles ta Najeriya ta ƙuduri aniyar doke Black Satellites ta ƙasar Ghana a wasan su na farko na rukuni na B a gasar WAFU B U20 Championship da za a buga a birnin Yamoussoukro na Cote d’Ivoire a ranar Litinin.

Kocin Flying Eagles, Abdu Maikaba, ya bayyana cewa “Muna neman nasara kai tsaye a kan Ghana saboda manufar mu ita ce mu kare kofin da muke riƙe da shi. Dole ne mu fara neman nasara a wasannin mu tun daga rana ta farko har zuwa ƙarshe.”

Nasara a ranar Litinin za ta sanya zakarun Afirka sau 7,watau Najeriya, cikin kyakkyawan matsayi na shiga wasan kusa da na ƙarshe.

Har ila yau, Najeriya za ta fafata da Togo da kuma Burkina Faso a wasannin rukuni na B mai ƙungiyoyi 4.

Super Eagles za ta buga wasan ta na biyu na rukunin a ranar 30 ga watan Yuli da ƙasar Togo a filin wasa na Lycée Scientifique de Yamoussoukro; kafin wasan ƙarshe na rukuni da Burkina Faso a ranar 2 ga watan Augusta.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *