Kungiyar Kulawa da Tsaron Afirka (African Security Watch) ta karrama Rundunar Sojin Najeriya a matsayin Rundunar Soji ta Kasa Mafi Fice wajen Ayyukan Yaki da Ta’addanci a Afirka na shekarar 2025.
Wannan ya biyo bayan amincewa da gagarumar nasarar da rundunar ta samu a fagen fama, da kyakkyawan jagoranci na dabara, da kuma sadaukarwar da take yi ba tare da gajiyawa ba wajen yaki da ta’addanci da itifakin tashin hankali a fadin Najeriya.
Wannan lambar yabo tana nuna fitowar Rundunar Sojin Najeriya a matsayin babbar runduna a Afirka wajen Yaki da Ta’addanci da Daukan Matakai kan Yan Tawaye (CTCOIN).
Wannan ya nuna sakamakon shekaru da dama na gudanar da ayyuka na sirri na leken asiri wadNetwork, wadanda suka rage karfin kungiyoyin ta’addanci, da dawo da tsaro ga al’ummomin da abin ya shafa, da kuma ba da gudummawa ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyyar.
An mika wannan babbar lambar yabo ga Shugaban Ma’aikatan Sojin Kasa (COAS), Laftanar Janar Waidi Shaibu, a ranar Laraba a Babban Kalubalen Soji da ke Abuja.
Janar Teriworie Gagariga ne ya mika masa ita, bayan da shi da kansa ya karbo ta a madadin Rundunar Sojin Najeriya yayin bikin Bada Lambar Yabo ta African Security Watch da aka gudanar a Banjul, babban birnin kasar Gambiya.
- WAFU B U20: Fying Eagles za ta kara da Sparrow Hawks
- WAFCON: Yadda Scorchers suka gasa wa Super Falcons aya a hannu
- Tawagun maza da mata na Najeriya sun samu tikitin shiga Gasar Ƙwallon Kwando ta ƙasashen Afirka
Wannan karramawa ta sake tabbatar da irin kimar da Rundunar Sojin Najeriya ke da ita a matsayin kwararriyar cibiyar da take da babban juriya da kwarewa, wadda koyarwarta ta aiki, da gogewarta a fagen fama, da kyawawan dabi’unta na tsari ke ci gaba da zama abin koyi ga dakarun soji a fadin nahiyar Afirka.
Yayin da yake karbar lambar yabon, Shugaban Sojin Kasa (COAS) ya bayyana ta a matsayin abin alfahari da ke nuna bajinta, kwarewa, juriya, da kuma sadaukarwa mara misaltuwa ta jami’ai da sojojin Najeriya wadanda ke ci gaba da sadaukar da rayuwarsu wajen kare ikon Najeriya da kare lafiyar ‘yan kasarta.
Shaibu ya lura cewa lambar yabon tana tabbatar da ingancin dabarun yaki da ta’addanci (CTCOIN) na Rundunar Sojin Najeriya, sannan tana karfafa matsayinta na zama abin koyi a nahiyar wajen tunkarar kalubalen tsaro masu sarkakiya.
Shaibu ya sadaukar da lambar yabon ga dakarun soji jarumai wadanda suka rasa rayukansu a fagen fama domin kare kasa, da kuma iyalansu wadanda goyon bayansu na gaskiya yake da matukar kima.
Shugaban sojin ya jaddada cewa jajircewarsu da hidimar da suke yi wa kasa ba tare da son kai ba, sune ke ci gaba da zaburar da Rundunar Sojin Najeriya wajen tabbatar da tsaron kasa da kuma dorewar zaman lafiya ga dukkan ‘yan Najeriya.
Bugu da kari, shugaban sojin ya sake jaddada kudirin Rundunar Sojin Najeriya na dorewa da nasarorin da ta samu ta hanyar inganta ayyukan sirri na leken asiri, da karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro daban-daban, da gudanar da horo mai tsanani, da inganta jin dadin ma’aikata, gami da mallakar kayan aiki na zamani.
Ya sake nanata cewa Rundunar Sojin, a karkashin jagorancinsa, za ta ci gaba da samun sauye-sauye domin zama kwararriya, mai saurin sabawa da yanayi, mai shirin yaki, da kuma runduna mai juriya da za ta iya magance kalubalen tsaro na Najeriya cikin gaggawa, yayin da take ba da gagarumar gudummawa ga zaman lafiya da tsaro a shiyyar baki daya.
A cewar kungiyar African Security Watch, Rundunar Sojin Najeriya ta samu wannan lambar yabo ta nahiyar ne sakamakon gagarumar nasarar da ta samu a ayyukan hadin gwiwa, da kamfen na leken asiri, da ingantaccen hadin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula, da bunkasa dakarun soji da gina kwarewa; wadanda duka suka raunana kungiyoyin ta’addanci tare da inganta tsaron kasa da na shiyyar.
Kungiyar ta kara da cewa, Rundunar Sojin Najeriya ta kafa kanta a matsayin ma’aunin kwarewa da ingancin aiki a fagen yaki da ta’addanci a fadin Afirka.