Ministan Harkokin wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan, ya jaddada buƙatar samun haɗin kan Musulmi yayin da ake fuskantar ƙalubale a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis yayin wani taron Majalisar Ministocin Harkokin waje, na Ƙungiyar haɗin kan Musulunci (OIC).

Bin Farhan ya sake tabbatar da goyon bayan kasar Saudiyya na dogon lokaci ga ƙudurin samar da kasar Falasɗinu, tare da yin Allah-wadai da yawan kutsen da ake yi a Masallacin Ƙudus.

Haka kuma, ya bayyana goyon bayan sa ga ƙarfafa Ƙungiyar Haɗin Kan Musulunci (OIC) da kuma habbaka rawar da take takawa wajen tunkarar ƙalubalen da ke addabar yankin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *