Ma’aikatar Kuɗin ta tarayya ta ce tattalin arzikin Najeriya na ci gaba da ƙaruwa, bayan alkaluman kashi na biyu na shekarar 2026 sun nuna cewa ainihin GDP ya karu da kashi 4.43 cikin 100 idan aka kwatanta da makamancin lokacin shekarar 2025.
Sanarwar da ma’aikatar ta fitar a Abuja ta ce wannan ƙaruwa ya haɓaka matsakaicin ci gaban tattalin arzikin ƙasar a rabin farko na shekarar 2026 zuwa kashi 4.16 cikin 100, daga kashi 3.68 cikin 100 da aka samu a rabin farko na shekarar 2025.
Ma’aikatar ta ce ci gaban ya fara bazuwa zuwa sassa daban-daban na tattalin arziki, inda ƙananan sassa 27 suka samu ci gaban sama da kashi 3 cikin 100 a kashi na biyu na shekarar, sabanin 23 a makamancin lokacin bara.
- Jamus zata rufe ofishin jakadancin Rasha dake Bonn
- Tinubu ya yi maraba da ƙaruwar tattalin arzikin Najeriya
A bangaren masana’antu, masana’antu sun samu ci gaban kashi 3.24 cikin 100, yayin da noma ya karu da kashi 4.39 cikin 100. Bangaren ayyuka kuwa, wanda shi ne mafi girman ginshiƙin tattalin arzikin ƙasar, ya samu ci gaban kashi 4.60 cikin 100.
Ma’aikatar ta kuma ce darajar naira ta samu ɗan ƙarfafa, inda ta nuna cewa naira ta ƙaru da sama da kashi 12 cikin 100 tsakanin rabin farko na shekarar 2025 da na 2026.
A cewarta, hakan ya taimaka wajen haɓaka girman tattalin arzikin Najeriya da kusan kashi 17 cikin 100 idan aka auna shi da dalar Amurka.
Gwamnatin Tarayya ta ce idan aka ci gaba da samun daidaiton tattalin arziki, da ƙaruwa a sassan samar da kaya da ayyuka da kuma ingantaccen yanayin saka hannun jari, Najeriya na da damar ci gaba da rike matsayinta cikin manyan tattalin arzikin Afirka tare da cimma burin gina tattalin arzikin da darajarsa ta kai dala tiriliyan ɗaya nan da shekarar 2030.
Sai dai gwamnatin ta jaddada cewa akwai buƙatar ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki tare da tabbatar da daidaiton manufofi, domin fa’idodin ci gaban tattalin arzikin su isa ga gidajen al’umma.