Zakaran Afirka, wato tawagar D’Tigress ta Najeriya, ta isa birnin Berlin na Jamus gabanin fara Gasar Cin Ƙwallon Ƙwando ta Mata ta Duniya.
Jakadan Najeriya a Jamus, Sanata Ita Enang, tare da wasu jami’an ofishin jakadancin Najeriya da ke babban birnin Jamus ne suka tarbi tawagar.
-
FIFA ta amince da murabus ɗin Gusau da kuma sabon tsarin NSC
-
Gabriel Jesus ya koma Barcelona da taka leda daga Arsenal
-
Enugu Rangers ta tashi 1-1 da Katsina United, Barau FC 3-1 Nasarawa United…
Zuwan nasu shi ne mataki na ƙarshe na shirye-shiryen gasar, wadda za a gudanar daga ranar 4 zuwa 13 ga watan Satumba na shekarar 2026 a Berlin.
D’Tigress, wadda ke riƙe da kambun zakaran Afirka bayan lashe Gasar FIBA ta mata ta AfroBasket karo na biyar a jere, za ta buga a rukunin B tare da Faransa, da Koriya ta Kudu da kuma Hungary.
