Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International ta buƙaci gwamnatin Najeriya da ta gudanar da bincike mai zaman kansa, cikin adalci da gaskiya kan zarge-zargen take haƙƙin ɗan Adam da aka aikata a yankin Kudu maso Gabas tsakanin shekarun 2016 zuwa 2025.
Ƙungiyar ta yi wannan kira ne a wani gangamin wayar da kai da nuna goyon baya da ta gudanar a Awka na jihar Anambra, domin neman adalci ga mutanen da rikicin yankin ya shafa.
- Moroko ta cire mai masaukin baki Canada daga gasar Cin Kofin Duniya
- Iran na nuna saƙon ci gaba da ramuwar gayya a taron bankwana da Khamenei
Da yake gabatar da rahoton ƙungiyar, Maurice Chukwu ya ce daga watan Janairun 2021 zuwa Disamban 2024, yankin ya fuskanci kashe-kashe ba bisa ƙa’ida ba da hare-hare da azabtarwa da ɓacewar mutane da kama mutane ba bisa ƙa’ida ba da kuma tauye ‘yancin zirga-zirga.
Yankin Kudu maso Gabas ya jima yana fuskantar hare-haren ta’addacci duk da ƙoƙarin da hukumomin tsaro ke yi na shawo kan matsalar.