Ƙungiyar Amnesty International ta ce wajibi ne a hukunta duk masu hannu a take haƙƙin ɗan Adam a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya, ko jami’an tsaro ne ko kuma wasu ƙungiyoyi masu ɗauke da makamai.
Ƙungiyar ta bayyana hakan ne yayin wani gangamin neman adalci da aka gudanar a Awka na jihar Anambra, inda jami’an tsaro da ɗalibai da ƙungiyoyin farar hula da lauyoyi da jami’an gwamnati da kafafen yaɗa labarai suka halarta.
- Amnesty ta buƙaci a yi bincike kan take haƙƙin ɗan Adam a kudu maso gabas
- Masu bauta da aka sace a Ekiti sun shaƙi iskar ‘yanci
Ta ce dakarun tsaro da ƙungiyar Ebube Agu da waɗanda ake kira ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba, da kuma mambobin IPOB da reshenta na ESN na daga cikin ɓangarorin da ake zargi da aikata take haƙƙin ɗan Adam, tana mai jaddada cewa bincike mai zaman kansa da adalci ne kaɗai zai tabbatar da gaskiya.