Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami’anta sun ceto wata mata mai suna Adijat Kuburat mai shekaru 43 tare da ɗanta Abdul Malik Hamzat mai shekaru biyu, bayan da masu garkuwa da mutane suka sace su a jihar Kwara.

A cikin wata sanarwa, rundunar ta ce jami’an sashen tattara bayanan sirri na FID-IRT tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro na al’umma sun kai samame a wani daji da ke Bode Sadu a ranar Asabar bayan samun sahihan bayanan sirri kan inda aka tsare mutanen.

Sanarwar ta ce masu garkuwar sun buɗe wa jami’an wuta da suka hango su, sai dai jami’an sun mayar da martani, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa cikin dajin, kafin daga bisani aka ceto matar da ɗanta.

Rundunar ta ƙara da cewa an kai waɗanda aka ceto asibiti domin kula da lafiyarsu, yayin da ake ci gaba da farautar waɗanda suka tsere domin gurfanar da su a gaban shari’a.

Babban Sufeton ‘Yan Sandan Najeriya, Olatunji Rilwan Disu, ya yaba da ƙwazon jami’an da suka gudanar da aikin, yana mai jaddada cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata miyagun laifuka a faɗin ƙasar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *