Babban Hafsan Tsaron Najeriya, Janar OO Oluyede, ya bayyana cewa ƙulla ƙarin alaƙa da Masarautar Saudiyya a fannin tsaro zai taimaka wajen inganta sha’anin tsaro a Najeriya tare da ƙara ƙarfafa ƙwarewar rundunonin tsaron ƙasar.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne yayin da yake karɓar bakuncin Jakadan Masarautar Saudiyya a Najeriya, Yousef bin Mohammed Al-Balawi, wanda ya kai ziyara Hedikwatar Tsaron Najeriya domin tattauna hanyoyin zurfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin ƙasashen biyu.

Babban Hafsan Tsaron ya jaddada muhimmancin dangantakar Najeriya da Saudiyya, yana mai cewa ya kamata a ci gaba da faɗaɗa hanyoyin haɗin gwiwa musamman a fannonin da za su ƙara inganta ƙarfin aiki da kwarewar Rundunonin Sojin Najeriya.

A nasa jawabin, Jakadan Saudiyya a Najeriya, Yousef bin Mohammed Al-Balawi, ya bayyana Najeriya a matsayin muhimmiyar ƙawa ga ƙasarsa a nahiyar Afirka, inda ya sake jaddada aniyar Saudiyya ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da Najeriya musamman a ɓangaren tsaro da soja.

Ya ce ƙarfafa hulɗar hukumomi da ƙwarewa tsakanin rundunonin tsaron ƙasashen biyu zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da suka shafi ƙasashen.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *