Iyalan tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i sun koka game da yadda suka ce shari’ar da ake masa na daukar sabon salo.
Da take bayani gaban manema labarai a helkwatar tsaro ta farin kaya, mai dakin tsohon gwamnan Hajiya Asiya El-Rufa’i, ta ce bayan bayar da belin sa a yau hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta dauke shi zuwa ofishin ta inda yaki sauka daga mota.
Hajiya Asiya ta ce daga nan ne jami’an na DSS suka dauke shi zuwa hukumar ICPC wanda daga nan ne suka sake komawa babbar kotu, bayan bayar da belin sa da sanyin safiya, daga bisani ta dage sauraron karar zuwa karfe 1 na rana.
Iyalan tsohon gwamnan sun nemi a gaggauta cigaba da sauraron karar domin yanke hukunci akan duk laifin da aka same shi da aikatawa, bawai cigaba da tsare shi har tsawon kwanaki sama da 80.
Da suke bayyana ra’yin su game da belin sa da kotu ta bayar, iyalan sun koka kan yadda suka ce sharuddan sunyi tsauri, domin babu wani babban jami’in gwamnatin da zai yi ganganci bayyana abubuwan da aka nema domin cika sharuddan.
Da yake jawabi a madadin Iyalan sa, Sanatan Kaduna ta tsakiya Lawal Adamu Usman yayi kira da a gaggauta sakin tsohon gwamnan.
“kamar yadda ya kai kansa hukumar EFCC, bai kamata ace har yanzu ana rike dashi ba”. inji sanata Lawal Adamu
Sanatan ya ce idan hukumomi na zargin Malam Nasiru El Rufa’i da taka dokar kasa kamata yayi ayi masa hukunci dai dai da abin da ya aikata, bawai cigaba da tsare shi ba wanda tamkar take masa hakkin kasancewar sa dan kasa ne.
Da sanyin safiyar Litinin 18 ga watan Mayun 2026 ne Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta amince da bukatar bayar da belin Malam Nasir El-Rufai tare da gindaya sharudda, wadanda iyalan sa ke ganin sunyi tsauri matuka.
