Wasu 'Yan Majalisar na cewa Shugaba Tinubu na da abin faɗa game da ƙin sakin kuɗaɗen na ayyukan mazaɓu

Majalisar Wakilai ta yi fatali da ƙudurin neman a gayyaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya yi bayani kan zargin rashin sakin kuɗaɗen ayyukan mazabu a faɗin ƙasar.

Ƙudurin, wanda ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Aba ta kudu da arewa a jihar Abia, Alex Mascot Ikwechegh na jam’iyyar LP, ya gabatar, ya nemi Shugaban ƙasar ya bayyana gaban majalisar kan jinkirin da ake samu wajen samar da kuɗaɗen ayyukan mazaɓu.

Sai dai ƙudurin ya haifar da muhawara mai zafi a zauren majalisar, inda ɗan majalisar APC daga jihar Plateau, Yusuf Gagdi, ya nuna adawar ƙarara, yana mai ra’ayin babu wani dalili da zai kai ga gayyatar shugaban ƙasa.

Da yake yanke hukunci, Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya ce buƙatar gayyatar Shugaba Tinubu ba ta cikin ainihin ƙudurin da aka gabatar, saboda haka ya bayyana ta a matsayin wadda ta saɓa da ƙa’idojin majalisar.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *