Tawagar ƙwallon kwando ta maza ta Najeriya, D’Tigers, ta doke Guinea da ci 80-79 a gasar neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya ta FIBA ta 2027 ta yankin Africa da aka buga a Luanda, Angola.
Wannan nasara mai ban mamaki ta tabbatar musu da shiga zagaye na biyu na samun tikitin zuwa gasar cin kofin duniya ta FIBA ta 2027 da za a buga a Qatar.
-
Tennis: Sabalenka za ta kara da Osaka a gasar Wimbledon
-
Colombia ta fitar da Ghana a gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
Kuma ita ce nasara ta biyu a jere ga Najeriya a wannan zagayen bayan sun doke Tunisia da ci 84-81 a ranar Alhamis, inda suka kammala da nasarori 2 ba tare da shan kashi ba a ƙarƙashin sabon kocin su David Fizdale.
Yanzu hankali ya koma kan wasan ƙarshe na Najeriya a wannan zagaye da za su buga da Rwanda, inda D’Tigers za su yi ƙoƙarin ci gaba da rike nasarorin su tare da ƙarfafa matsayinsu kafin fara sabon mataki na neman tikitin.