Jhon Arias ne ya ci kwallon da ta baiwa Colombia nasara yayin da ta doke Ghana da ci 1-0 a birnin Kansas a ranar Juma’a, don kaiwa zagaye na 16 na gasar Cin Kofin Duniya ta 2026.
Arias ya zura ƙwallon ne a minti na 14, inda hakan ya tsawaita tarihin rashin shan kashi, tare da tabbatar da haduwa da Switzerland a zagaye na 16.
-
Cape Verde ta girgiza duniya duk da ficewa daga gasar cin kofin duniya
-
Kano Pillars ta naɗa Daniel Ogunmodede a matsayin sabon kociyanta
Colombia ta shiga gasar ba tare da an ba ta kulawa sosai ba, duk da cewa ba tayi rashin nasara ba a kan Portugal da Uzbekistan da DR Congo yayin da ta zama na daya a rukuni na K.
Los Cafeteros sun zama tawaga ta hudu daga kudancin Amurka da ta kai zagaye na 16, suna tare da Paraguay mai abin mamaki wadda ta doke Jamus, tare da Brazil da Argentina, wadanda suma suka tsira daga firgici a wasanninsu.