Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta saki wani mutum mai suna Nura Idris, bayan ta tsare shi bisa zargin alaƙa da ƙungiyar Boko Haram.
Daraktan Hukumar ta (DSS) Oluwatosin Adeola Ajayi, ne ya bayar da umarnin a ranar Asabar, bayan rahoton kwamitin da aka kafa domin sake duba shari’ar da aka yi masa, ya tabbatar da cewa babu wata hujja da ke alaƙanta shi da ƙungiyar.
Daraktan ya kuma umarci a baiwa matashin tallafin Naira miliyan Uku, domin taimaka masa farfaɗo da rayuwar da kasuwancin sa.
- 2027: Gwamnatin Tinubu na yin duk mai yiwuwa domin ta hana ni takara – Peter Obi
- Hukumar kula da cutuka masu saurin yaɗuwa na ƙara tsaurara matakai a Najeriya
A wani bincike da hukumar tsaron ta gudanar, ta gano cewar matashin ɗan asalin ƙaramar hukumar Soba a jihar Kaduna, yana sana’ar noma da kiwo ne, gabanin kama shi a watan Yunin shekarar 2024.
A baya bayan nan dai hukumar tsaron ta kafa wasu kwamitoci dake sake nazari kan shari’o’i sama da 30, domin tabbatar da adalci ga waɗanda ta kama.
Kawo yanzu, rahotanni daga hukumar sun tabbatar da biyan diyyar fiye da Naira Miliyan 300, ga waɗanda ta kama kuma aka yankewa hukunci, akan laifukan da basu aikata ba.