Kungiyoyin ‘yan tawaye a Mali sun ɗauki alhakin kai jerin hare-haren da aka kai a kan aƙalla sansanonin soji 7 a faɗin ƙasar a ranar Asabar.

A cikin wata sanarwa, reshen ƙungiyar Al-Qa’ida, Jama’at Nusrat al-Islam wal Muslimin (JNIM) ta ce ta kuma karɓe aƙalla 3 daga cikin waɗannan sansanonin.

Majiyoyin tsaro da na soji, da mazauna yankin sun ce ‘yan tawayen da takwararsu ta Azawad Liberation Front (FLA) ƙarƙashin jagorancin ‘yan Tuareg sun kai hari kan garuruwa da dama da kuma gidan yari a farmakin da ya fara da misalin karfe 5 na asuba.

Waɗannan hare-hare sun zo watanni ka ɗan bayan FLA da JNIM sun kai hari tare kan hukumomin soji wanda ya shafi tashi da sauka na jirgin sama na Bamako da ya yi ajalin ministan tsaron ƙasar.

Sojojin Mali sun bayyana cewa sun “daƙile hare-haren na ranar Asabar kuma lamarin yanzu na ƙarƙashin cikakken kulawarsu.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *