Rundunar Sojin Ƙasa ta Najeriya da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarsu domin inganta shirin tunkarar iftala’i da bayar da agajin gaggawa, musamman dangane da barazanar ambaliyar ruwa a sassan ƙasar.
Shugaban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu ne, ya bayyana hakan yayin da ya karɓi bakuncin Babbar Daraktar hukumar NEMA, Hajiya Zubaida Abubakar Umar, a hedikwatar rundunar dake Abuja.
Ya ce rundunar sojin ta kafa ƙungiyoyin bayar da agajin gaggawa a dukkan shiyyoyin shida na ƙasar domin gaggauta kai ɗauki ga yankunan da ke fuskantar haɗarin ambaliya da sauran iftala’i.
- ‘Yan Sandan Abuja sun ceto mutane huɗu da aka yi garkuwa da su bayan musayar wuta da masu garkuwa
- NEMA ta ce jihohi 33 na fuskantar barazanar ambaliyar ruwa
Haka kuma ya umurci Babban Jami’in Horaswa na rundunar da ya bai wa hukumar NEMA damar amfani da cibiyar horas da jami’anta domin gudanar da atisayen haɗin gwiwa da shirye-shiryen tunkarar bala’o’i.
Shaibu ya jaddada muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro da na agajin gaggawa, inda ya bayyana cewa hakan ne zai taimaka wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.