Shugaban Amurka Donald Trump ya yi wa Iran barazana bayan rahotannin da ke cewa an yi kira a fili da a kashe shi yayin jana’izar jagoran addinin Iran da aka kashe, Ayatollah Ali Khamenei.

Haka kuma, Isra’ila ta ce ta gano wani sabon shirin Iran na kashe Trump.

A wani saƙo da ya wallafa a dandalinsa na Truth Social yau Asabar, Trump ya ce Amurka ta tanadi makamai masu linzami dubu guda da ke nufar Iran.

Ya ce idan gwamnatin Iran ta yi yunƙurin kashe shugaban Amurka, sojojin ƙasar za su mayar da martani ta hanyar lalata manyan wurare a Iran.

Rahotanni daga kafafen yaɗa labarai na Amurka sun bayyana cewa Isra’ila ta miƙa wa Washington bayanan sirri kan wani sabon shiri da Iran ke yi na kashe Trump.

CNN da Wall Street Journal sun ce bayanan sun nuna cewa barazanar ta kasance sabuwa kuma ana kallonta a matsayin mai matuƙar muhimmanci.

Iran ta daɗe tana zargin Trump tun bayan umarnin da ya bayar a shekarar 2020 na kashe babban kwamandan dakarunta, Janar Qassem Soleimani, ta hanyar harin jirgin sama marar matuƙi.

Rahotanni sun ce wannan sabuwar barazana ta sa Hukumar Tsaron Shugaban Amurka ta ba Trump shawarar canza jirgin da zai hau bayan taron NATO.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *