Tawagar 'yan wasan Super Eagles ta Najeriya

Tawagar ƙwallon ƙafa ta Najeriya Super Eagles, ta  taya ƙasar Sifaniya murnar lashe Gasar cin Kofin Duniya na shekarar 2026.

Cikin wani sako da Super Eagles ta wallafa a shafin ta na X jim kaɗan bayan Sifaniya ta doke zakarun da ke riƙe da kofi, Argentina, da ci 1-0 a wasan ƙarshe na ranar Lahadi, ta yi alƙawarin dawowa gasar a shekarar 2030.

“Muna taya ƙasar Sifaniya murnan lashe Gasar Cin Kofin Duniya na 2026… Sai mun hadu a 2030.”

A na sa ran cewa wannan saƙon zai kawo ƙarshen rashin halartar Najeriya Gasar, bayan ta kasa samun tikitin shiga gasar karo na biyu a jere.

Najeriya ta rasa damar shiga gasar ne bayan ta sha kayi a hannun Jamhuriyyar Kongo a birnin Rabat na Moroko,  inda Najeriya ta sha kayi da ci 4-3 a bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Wannan ya ƙara tsawaita rashin halartar ta na shekaru 8 bayan ta gaza halartar wasan a shekarar 2022 da ƙasar Qatar ta karɓi baƙunci.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *