Hukumar Kiyaye Haɗura ta Kasa (FRSC) ta ƙaddamar da wani samamen musamman na tsawon kwana uku a jihohin Sokoto da Kebbi da Zamfara domin yaki da maƙare kaya fiye da kima da haɗa kaya da mutane waje guda, da sauran laifukan da ke janyo hatsarin hanya.

Wannan samame, mai taken “Daidaita Lodi” da “Lodi Limit,” ana gudanar da shi ne a lokaci guda a duk shiyyoyi 12 na hukumar a fadin kasar domin inganta kiyaye dokokin tsaron hanya.

Yayin da yake jawabi gurin ƙaddamar da shirin a Sakkwato, Kwamandan Shiyya, mataimakin kwamandan hukumar (ACM) Shaba Bariam Akanbi, ya bayyana cewa wannan motsi ya biyo bayan umarnin Shugaban Hukumar na Kasa, Shehu Mohammed, na karfafa tsaurara dokoki a kan ayyukan hanya masu haɗari.

Ya bayyana cewa samamen zai maida hankali ne a kan maƙare lodi fiye da ƙima, ɗaukar fasinjoji tare da kaya da toshe hanyoyi, da sauran laifukan kiyaye hanya, yayin da gargadi da wayar da kan jama’a zai tafiya tare da aiwatar da doka.

Kwamishinan Sufuri na Jihar Sakkwato, Bala Kokani Kebbe, ya bayyana yaƙin neman zaɓen a matsayin wanda ya zo a kan gaba, inda ya kiyaye cewa lodin fiye da kima yana ɗaya daga cikin manyan dalilan da ke sa hatsuran hanyoyi da za a iya kiyayewa.

Ya tabbatar wa FRSC samun goyon bayan gwamnatin jihar wajen aiwatar da dokokin cunkoson ababen hawa domin kare rayuka da dukiyoyi.

Da yake wakiltar Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, Dan Iyan Sakkwato, Aminu Bala, ya alkarta goyon bayan Majalisar Sarkin Musulmi ga kamfen din kiyaye haɗurra a hanya, tare da yi wa masu ababen hawa gargadi da su kiyaye dokokin hanya.

Tun da farko, Kwamandan Shiyya na Jihar Sakkwato na FRSC, Adamu Argungu, ya yi gargaɗin cewa wadanda aka kama yayin samamen za a gurfanar da su a gaban Kotun Tafi-da-Gidanka (Mobile Court).

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *