Pep Guardiola, tsohon kocin Manchester City

Kafar Sky ta Italiya ta ruwaito cewa Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Italiya, FIGC, ta tattauna da tsohon kocin Manchester City, Pep Guardiola, domin shawo kansa ya zama sabon kocin tawagar ƙasar.

Rahotanni sun ce tsohon ɗan wasan Italiya Paolo Maldini tare da Leonardo, sun gana da Guardiola a Barcelona kwanaki uku baya.

Tsoffin ‘yan wasan Italiya Roberto Mancini da Andrea Pirlo suma suna cikin waɗanda ake tunanin za su iya samun aikin.

Idan Guardiola ya karɓi aikin zai zama mutum na biyu wanda ba ɗan ƙasar Italiya ba da zai horas da tawagar ƙasar kuma na farko tun daga shekarun 1960.

Guardiola ya shafe shekaru 10 ya na horaswa a filin wasa na Etihad.

Guardiola mai shekaru 55, ya na iya magana da harshen Italiya kuma ya yi shekaru biyu yana buga ƙwallo a Serie A ta Italiya, daga 2001 zuwa 2003, tare da buga wa Brescia sau biyu da Roma sau ɗaya.

A cikin shekaru goma da ya yi a Ingila, Guardiola ya lashe kofuna 20, ciki har da gasar Firimiyar Ingila sau 6, FA Cup sau 3, League Cup sau 5 da Community Shield sau 3.

Haka kuma ya lashe Gasar Zakarun Turai a 2023, sannan ya biyo baya da UEFA Super Cup da FIFA Club World Cup.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *