Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) ta yi barazanar komawa yajin aikin da ta dakatar da a faɗin ƙasar sakamakon ƙin biyan albashi da kuma rashin cika yarjejeniyar shekarar 2025 yadda ya kamata.
Shugaban ƙungiyar na ƙasa, Christopher Piwuna, shi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya rarraba wa manema labarai a ranar Juma’a a Abuja, bayan taron gaggawa na Majalisar Gudanarwa ta Ƙasa (NEC).
Piwuna ya bayyana cewa yarjejeniyar da aka ƙulla tsakanin Gwamnatin Tarayya da ASUU a watan Disamban 2025—wadda aka cimma bayan shafe fiye da shekaru takwas ana fafutuka—Gwamnatin Tarayya da jihohi da dama sun gaza aiwatar da ita yadda ya kamata.
Ya ce wannan yanayi ya jefa malaman jami’a a cikin rashin tabbas game da albashinsu da sauran haƙƙoƙinsu, tare da gargadin cewa matuƙar ba a ɗauki matakin warware matsalolin ba, za a iya sake tsunduma cikin sabon yajin aikin a faɗin ƙasar.
“Sai dai idan an ɗauki matakan gaggawa masu ɗorewa domin warware matsalolin da suka shafi jin daɗi da rayuwar malaman jami’o’in Nijeriya, ASUU-NEC ba za ta ɗauki alhakin komai ba,” in ji Piwuna.
Ya ƙara da cewa ƙungiyar za ta iya kiran mambobinta zuwa “yajin aikin gargaɗi a faɗin ƙasar nan da ɗan ƙanƙanin lokaci” muddin gwamnati ta gaza magance waɗannan tanadi cikin nasara.
-
Wacce rawa Ƙasar Jordan ke takawa a rikicin Gabas ta Tsakiya
-
FRSC ta ƙaddamar da yunƙurin kawo ƙarshen lodin wuce kima
-
Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama mutum biyu bisa zargin kisa
Piwuna ya bayyana cewa har yanzu gwamnati ba ta biya albashin watanni uku da rabi ba daga cikin watanni bakwai da rabi da gwamnatin Buhari ta riƙe, duk da biyatar watanni huɗu da Shugaba Bola Tinubu ya yi.
“Muna masu takaicin sanar da cewa babu abin da ya sauya game da albashin watanni uku da rabi da aka zaɓe aka bari na gwamnatin Buhari tun lokacin da muka yi jawabi ga jama’a na ƙarshe,” in ji shi.
Tsohon shugaban ya ce wannan albashi da aka riƙe ya jefa malamai cikin ƙuntatawar kuɗi da ta hankali, yayin da ƙarfin sayen kayayyaki na kuɗin ya ragu sosai tun lokacin da aka sami albashin.
Piwuna ya kuma nuna damuwa kan biliyoyin na’ira da aka cire daga albashin malamai domin fensho, ƙungiyoyin haɗin gwiwa (cooperative), da kuɗaɗen gudunmawar ASUU (check-off dues), amma aka ƙi tura su ta hanyar da ta dace har na tsawon watanni.
“ASUU-NEC a shirye take ta kira mambobinta matuƙar ba a ɗauki matakin azo-a-gani ba wajen magance wannan matsala da ta daɗe tana ci mana tuwo a ƙwarya ba tare da ɓata lokaci ba,” in ji Piwuna.
Shugaban na ASUU ya yaba wa Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti, da sauran gwamnonin da suke aiwatar da yarjejeniyar shekarar 2025, inda ya ƙurajen jihohin da ba su fara ba da su gaggauta yin hakan don kauce wa rikicin ma’aikata.
Tsohon ya caccaki Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, kan ƙarin wa’adin shekaru biyu da ya yi wa Mataimakin Shugaban Jami’ar Jihar Osun (VC), Prof. Clement Adebooye, yana mai bayyana hakan a matsayin wani abu da ya saɓa wa dokar jami’a.
Ya ce wannan mataki na iya shafar cin gashin kanta na jami’a tare da dawo da al’adun da ba su dace ba game da ƙarin wa’adin aiki, inda ya buƙaci Adeleke da ya sake tunani a kan wannan shawara.
Haka zalika, Shugaban ASUU ya goyi bayan kiran da Shugaban Ƙungiyar Kwadago ta Ƙasa (NLC), Joe Ajaero, ya yi na a gaggauta sake duba Ƙaramin Albashi na Ƙasa domin rage raɗadin ƙuncin tattalin arziki da ke ƙaruwa.