An naɗa tsohon kocin Najeriya na ‘yan ƙasa da shekaru 20, Aliyu Zubairu, a matsayin sabon kocin ƙungiyar ƙasar Sudan, Al Ahli Madani, kan kwantiragin shekaru biyu.
Aliyu ya maye gurbin Farouk Jabra, kuma ya zama sabon koci daga Najeriya da ya karɓi ragamar ƙungiyar na nahiyar Afirka.
An sanar da naɗin Zubairu ne sa’o’i kadan bayan ya tabbatar da rabuwa da ƙungiyar Telecom SC na gasar firimiya ta biyu ta ƙasar Masar bisa yardar juna.
-
Bayan doke Switzerland 3-1, Argentina za ta fafata da Ingila a wasan kusa da na ƙarshe
-
Najeriya ta samu tikitin shiga Gasar Cin Kofin Duniya na mata ‘yan ƙasa da shekaru 17 na 2026
-
Zadok Yohanna ya shiga cikin ‘yan takara 100 na kyautar Golden Boy ta 2026
Da yake jawabi bayan kammala yarjejeniyar zuwa Sudan, koci Zubairu ya ce wannan babbar dama ce gare shi a cikin aikinsa.
“Al Ahli Madani babbar ƙungiya ce mai tarihi. Ina fatan yin aiki tare da ‘yan wasa, da masu gudanarwa da magoya baya domin cimma burinmu, musamman yanzu da ƙungiyar ke shirin buga Gasar Cin Kofin Confederation ta CAF,” in ji Zubairu.
Wannan mataki wata babbar nasara ce ga Zubairu, wanda tarihin aikinsa na kociya ke ƙara girma a Afirka.
Tsohon kocin ya taɓa jagorantar Wikki Tourists da Gombe United da El-Kanemi Warriors a gasar Firimiya ta Najeriya, kafin ya kai ga komawa Telecom SC.
