Rundunar Sojan Operation Fansan Yamma, sun dakile jerin hare-haren garkuwa da mutane a jihar Zamfara, inda suka ceto shugaban kwalejin kimiyya da fasaha ta Kauran Namoda, Dakta Aminu Yusuf, tare da wasu fararen hula.
Rundunar haɗin gwiwar ta ce lamarin ya faru ne da sanyin safiyar ranar 28 ga Yuli, 2026, bayan da ta samu kiran gaggawa kan harin da ‘yan ta’adda suka kai a titin Tsohon-Tasha da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda.
Ta ce maharan sun kai hari gidan shugaban kwalejin, inda suka kashe jami’in tsaron sa, tare da raunata wani mutum guda, kafin su yi ƙoƙarin yin garkuwa da Dakta Aminu Yusuf da iyalansa.
- A karon farko an zabi mace ta shugabanci Majalisar Dokokin Aljeriya
- Ba’a Babban Birnin Tarayya aka kaiwa Jami’in Soja hari ba-CP Ahmed
Haka kuma a yankin Tungan Dorawa da ke Barkeji, sojojin sun dakile wani yunƙurin garkuwa da mutane, inda suka ceto fitaccen ɗan kasuwa, Alhaji Azaria, da wasu mutane 21 da aka sace.
Rundunar ta ce ta kama wani mutum mai suna Falalu Yusuf, mai shekaru 45, bisa zargin taimaka wa ‘yan ta’adda da bayanan sirri.
Operation Fansan Yamma ta ce za ta ci gaba da ƙarfafa ayyukan tsaro domin dawo da zaman lafiya a Zamfara da sauran sassan Arewa maso Yamma, tare da kira ga jama’a su ci gaba da bayar da bayanan da za su taimaka wajen dakile ayyukan masu aikata laifuka.