Hukumar Kula da Kare Haɗurra ta Ƙasa FRSC ta gano wasu motoci biyu da ake zargin an sace su a jihar Edo ta hanyar amfani da tsarin tantance motoci na NVIS.

Motar farko ita ce Toyota Highlander, inda binciken NVIS ya nuna cewa lambar rajistar da ke jikin motar ba ta dace da bayananta ba. Bayan amfani da lambar tantance mota ta musamman (VIN), an gano cewa an sace motar a Legas a watan Yunin 2025.

A wani bincike na daban, jami’an FRSC sun gano wata Toyota Venza wadda aka kawo domin tantancewa ba tare da lambar rajista ba. Binciken ya gano ainihin bayananta, inda mai ita ya tabbatar cewa an rasa motar tun watan Janairun 2026 a Sapele, jihar Delta.

Hukumar FRSC ta miƙa motocin biyu da waɗanda ake zargi zuwa sashen binciken manyan laifuka na ‘yan sandan jihar Edo domin ci gaba da bincike.

Shugaban FRSC, Shehu Mohammed, ya ce wannan nasarar ta nuna muhimmancin tsarin NVIS wajen gano motocin sata da tabbatar da mallaka da kuma yaƙi da laifukan da suka shafi motoci.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *