Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta tura Kwamishinan ‘Yan Sanda Samuel Erale Etaifo zuwa jihar Osun domin jagorantar tsare-tsaren tsaro gabanin zaɓen gwamnan jihar da ke tafe.

A cikin wata sanarwa, rundunar ta ce naɗin wani Kwamishinan ‘Yan Sanda na zaɓe (CP Elections) na daga cikin matakan tabbatar da zaman lafiya da tsaro da gudanar da sahihin zaɓe a jihar.

Sanarwar ta bayyana cewa CP Etaifo zai jagoranci daidaita ayyukan tsaro a lokacin zaɓen tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, domin kare masu kaɗa ƙuri’a da jami’an zaɓe da kayan aikin zaɓe.

Sai dai rundunar ta tabbatar da cewa Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar Osun, CP Ibrahim Gotan, zai ci gaba da kula da harkokin yau da kullum na rundunar a jihar, tare da bai wa CP na zaɓe dukkan goyon bayan gudanarwa da ayyukan tsaro.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *