Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce zai umarci dakarun Amurka da su dakatar da sabbin hare-hare kan Iran, yana mai cewa ƙawayen Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya sun cimma wasu muhimman ka’idojin yarjejeniya da za ta kawo ƙarshen yaƙin da ya shafe watanni biyar yana gudana.
Trump ya rubuta a wani saƙo da ya wallafa a kafar sada zumunta cewa yarjejeniyar da ake shirin cimma wa za ta ƙunshi “buɗe mashigar Hormuz gaba ɗaya cikin gaggawa, da kuma kawo ƙarshen barazanar nukiliyar Iran.”
- Jami’an Tsaron Nijar fiye da 10 sun mutu a harin Boko Haram a Diffa
- Mali: HRW ta zargi dakarun Africa Corps na Rasha da kashe fararen hula takwas
- A karon farko an zabi mace ta shugabanci Majalisar Dokokin Aljeriya
Trump ya taɓa sanar da dakatar da hare-hare kan Iran sau da dama tun bayan da Amurka da Isra’ila suka kai hari kan Iran a ranar 28 ga Fabrairu, saidai fadan yaci gaba da dawowa.
Sai dai ko a karshen makon nan an jiyo wani janar na sojin Amurka dake jagorantar sojin kasar a faɗan da takeyi da Iran na cewa ba su da isassun makamai da za su ci gaba da kai hare hare a yakin.