Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Jama’a, Mohammed Idris, ya taya tsohon Shugaban Mulkin Soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, murnar cika shekaru 85 da haihuwa, inda ya bayyana shi a matsayin dattijon ƙasa da rayuwarsa ta kasance muhimmin sashe na tarihin Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ministan ya ce tarihin Babangida na aikin soja da jagorancin ƙasa da kuma rayuwarsa a matsayin ɗan ƙasa mai kishin kasa, ya taka muhimmiyar rawa wajen sauye-sauyen siyasa da hukumomi a Najeriya.

Mohammed Idris ya ce duk da cewa Babangida ya bar mulki shekaru da dama da suka gabata, har yanzu yana ci gaba da bayar da gudunmawa kan batutuwan da suka shafi haɗin kan Najeriya da zaman lafiya da ci gaban ƙasa.

Ya bayyana kwarewar tsohon shugaban a fannin jagoranci da hidimar jama’a a matsayin wata taska da matasa da shugabanni na baya da masu zuwa za su iya koya daga gare ta wajen fahimtar ƙalubalen gina ƙasa.

Ministan ya kuma yaba da yadda Babangida ke nuna imani da Najeriya tare da ci gaba da yin kira da samar da haɗin kai da zaman lafiya tsakanin ’yan ƙasa.

Mohammed Idris ya ce, “Janar Babangida na ci gaba da kasancewa muhimmiyar murya a tafiyar ƙasarmu, kuma yayin da ya cika shekaru 85, muna murnar hidimarsa da dattijantakarsa da kuma jajircewarsa wajen ganin Najeriya ta kasance ƙasa ɗaya.”

Ministan ya yi wa tsohon shugaban fatan ƙarin shekaru masu yawa cikin koshin lafiya, zaman lafiya da walwala, tare da fatan ya ci gaba da samun ƙaunar iyalansa da mutunta ’yan Najeriya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *