Ambaliyar ruwa ta sake addabar wasu sassan Abuja sakamakon ruwan sama mai ƙarfi, lamarin da ya sake jawo hankalin jama’a kan yadda toshe hanyoyin ruwa da sauya wasu wuraren da aka ware domin korewar birni ke ƙara tsananta matsalar.
Ambaliyar ta shafi yankunan Wuse 2 da Mabushi da Lugbe da Gwarinpa da Wuye da Gudu da Nyanya da Asokoro da Maitama da wasu wurare, inda ruwa ya mamaye hanyoyi tare da jefa wasu mazauna da masu ababen hawa cikin wahala.
Wasu mazauna Abuja sun danganta matsalar da yadda ake gina gine-gine a wuraren da aka ware domin shakatawa kusa da hanyoyin ruwa, lamarin da suke cewa yana rage damar ƙasa na tsotse ruwan sama tare da ƙara yawan ruwan da ke gudana a kan tituna.
- FCTA na ɗaukar matakan magance ambaliyar ruwa a wasu sassan Abuja – Olayinka
- Kano – Almajirai huɗu sun mutu bayan cin gurɓataccen abinci
- Iran ta saka lada dala 30,000 kan kama ko kashe sojan Amurka
Haka kuma, zubar da robobi da leda da shara da sauran tarkace a magudanan ruwa na daga cikin abubuwan da ke hana ruwa samun hanyar wucewa yadda ya kamata.
Hukumomin kula da agajin gaggawa sun ce sun fara tantance wuraren da ambaliyar ta shafa tare da duba irin taimakon da mazauna ke buƙata.
Hukumar NEMA da FCT FEMA sun gudanar da aikin tantancewa a Wuse, Mabushi da wasu wuraren da ambaliyar ta shafa domin gano barnar da aka samu a gidaje da tituna da wuraren kasuwanci da sauran muhimman ababen more rayuwa.
Hukumomin sun kuma buƙaci mazauna wuraren da ke fuskantar barazanar ambaliya da su kasance cikin shiri, su guji shiga hanyoyin da ruwa ya mamaye, tare da bin shawarwarin jami’an tsaro da hukumomin agajin gaggawa.
Hukumar FEMA ta kuma gargadi masu ababen hawa da kada su yi ƙoƙarin tuƙi cikin ruwan ambaliya, saboda ba a san zurfin ruwan ba kuma ana iya samun ambaliyar bazata da za ta iya kwashe mutane ko motoci.
Hukumomin sun kuma bukaci mazauna Abuja da su riƙa tsaftace magudanan ruwa, su guji gina gine-gine a kan hanyoyin ruwa, tare da kai rahoton duk wani gini ko ci gaban da ke hana ruwa bin hanyarsa.