Rundunar ’yan sandan Jihar Sokoto ta ce ta kashe ’yan bindiga biyu tare da cafke wasu mutane tara da ake zargi da hannu a aikata laifuka daban-daban, ciki har da satar babura, garkuwa da mutane da kuma sauran laifukan ta’addanci.
Rundunar ta bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da Kakakin ’yan sandan Jihar Sokoto, DSP Ahmad Rufa’i, ya gudanar a ranar 19 ga Agusta, 2026, a madadin Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Hayatu Hassan Shaffa.
- An naɗa Farfesa Bashir Aliyu Umar shugaban NIFAC na ƙasar Ghana
- Tinubu ga jamio’i: ‘Ku maida da hankali kan ƙwarewa maimakon takardun shaidar karatu’
A cewar rundunar, a ranar 15 ga Agusta da misalin ƙarfe 9 na dare, an samu rahoton cewa wasu ’yan bindiga dauke da muggan makamai na kokarin kai hari kauyen Dankadu da ke karamar hukumar Illela, bayan sun taso daga dajin Tsauana.
Rundunar ta ce jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane da sauran jami’an tsaro sun hanzarta zuwa wurin, inda suka yi arangama da ’yan bindigar. Bayan musayar wuta mai tsanani, ’yan bindigar sun tsere zuwa cikin daji dauke da raunukan harbin bindiga.
Bayan jami’an tsaron sun binciki dajin, sun ce sun samu nasarar kashe biyu daga cikin ’yan bindigar tare da kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyu da harsasai 54