Shugaban Ƙasar Najeriya, Bola Tinubu, ya bayyana al’ummar Hausawa a matsayin “manyan ginshiƙai” waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kan Najeriya da ci gabanta.
Tinubu ya bayyana hakan ne a cikin saƙon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Laraba, domin taya al’ummar Hausawa murnar Ranar Hausa, wadda ake gudanar da bikin ta a sassan nahiyar Africa ta yamma.
Shugaban ƙasar ya ce harshen Hausa ya bunƙasa sosai, inda ya zama ɗaya daga cikin manyan harsunan haɗin kai da kasuwanci a faɗin duniya.
Ya ce: “Al’ummar Hausawa manyan ginshiƙai ne waɗanda ke taka muhimmiyar rawa wajen haɗin kan Najeriya da ci gabanta.
- ‘Yan sanda sun tsare jami’an tsaron Gwamnan Katsina a Abuja
- Bikin Maulidi: Kiristoci da Musulmai Sun Haɗu a Kaduna Domin Zaman lafiya
- Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta aikewa Kwamishinonin ta wani umarni
“Ina taya ɗaukacin al’ummar Hausawa murnar wannan rana ta Hausa, wadda ake bikin ta a fadar Daura mai tarihi a yau,” in ji shi.
Ranar Hausa, wadda ake kuma kira Ranar Hausa ta Duniya (World Hausa Day) ko Ranar Hausa, ana bikin ta ne a kowace shekara a ranar 26 ga watan Agusta.
An fara bikin ne a matsayin wani shiri na kafafen sada zumunta da wani ɗan jaridar Abdulbaki Aliyu Jari ya ƙaddamar, da nufin inganta amfani da harshen Hausa a intanet tare da wayar da kan jama’a game da muhimmancinsa al’adar hausawa.
Tun daga lokacin, bikin ya yaɗu zuwa ƙasashe daban-daban a Afirka, Turai, Gabas ta Tsakiya, Asiya da Amurka, duk da cewa har yanzu Majalisar Ɗinkin Duniya ba ta amince da shi a hukumance a matsayin wata rana ta duniya ba.
Hausa na daga cikin manyan harsunan da ake magana da su a Najeriya.
Haka kuma, yana daga cikin harsunan da aka fi amfani da su a Afirka, kuma yana cikin manyan harsunan duniya idan aka yi la’akari da yawan masu magana da shi.