Ibrahima Yakubu
Wani malamin addinin Kirista mazaunin Kaduna, Fasto Dokta Yohanna Buru, wanda ya karɓi lambar yabo ta mako-mako ta Majalisar Ɗinkin Duniya kan dacewar addinai na duniya (Interfaith Harmony week) daga hannun Sarki Abdullahi na ƙasar Jordan, ya nuna babban matakin haƙurin addini ta hanyar jagorantar mambobinsa don yin bikin taya murnar murnar Eid-el-Maulud tare da Musulmai a Jihar Kaduna domin ƙarfafa zaman lafiya da kyakkyawar fahimta tsakanin ƙungiyoyin addinai daban-daban.
Fasto Buru ya ce wannan shi ne karonsa na 11 yana shiga cikin bikin Maulidi na shekara-shekara tare da dubun-dubatar Musulmai a Jihar Kaduna da sauran sassan arewacin Najeriya.
Fasto Buru, Babban Jagora na Cocin Christ Evangelical and Life Intervention Ministry kuma wanda ya sami karɓuwa a duniya don haɗin kan addinai, ya ce bikin ya nuna shekararsa ta 11 a jere yana shiga cikin harkokin Maulidi tare da Musulmai a Kaduna da sauran sassan arewacin Najeriya.
Shugabannin Kiristan sun haɗu da dubun-dubatar Musulmai a filin taro na Murtala Mohammed Square da ke Kaduna, inda shugabannin addinai da mambobin al’umma suka taru domin tunawa da wannan lokac.
- ’Yan sanda sun tarwatsa maboyar ’yan bindiga a Kaduna
- Sama da ‘yan ta’adda 150 suka miƙa wuya a mako ɗaya
Da yake jawabi a wurin taron, Fasto Buru ya ce shigarsa ta samo asali ne saboda buƙatar inganta zaman tare cikin lumana, haƙurin addini, girmama juna da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin Kiristoci da Musulmai.
Ya ce bikin Maulidi yana ba da dama mai mahimmanci ga mutane na addinai daban-daban don su zo guda, su yi mu’amala kuma su fahimci juna, yana mai jaddada cewa zaman tare cikin lumana yana buƙatar tattaunawa da girmama juna.
Yayin da yake ba da lacca kan zaman lafiya da haɗin kai, Fasto Buru ya ce ya kamata a kalli Annabi Muhammadu (SAW) a matsayin manzo wanda koyarwarsa kan zaman lafiya, ƙauna, da tausayi ke da mahimmanci ga ɗan adam.
Ya ce, “Annabi Muhammadu (SAW) na dukkan ɗan adam ne, ba tare da la’akari da ƙabila, al’ada, yanki, launi, jinsi, ko ƙasa ba.
“Malamin addinin ya yi kira ga ‘yan Najeriya daga kabilu da addinai daban-daban da su rungumi juna, su yafe wa juna bambance-bambancen da suka gabata, sumni aiki tare don gina ƙasa mai zaman lafiya da haɗin kai.
A cewarsa, Kiristoci da Musulmai suna da imani guda ɗaya ga Mahalicci guda ɗaya kuma ya kamata su yi amfani da littattafansu masu tsarki, wato Littafi Mai Tsarki (Injila) da Alkur’ani, a matsayin jagora zuwa ga zaman tare cikin lumana.
Fasto Buru ya ce shigarsa cikin bukukuwan Maulidi ba ya shafar addininsa na Kirista, yana mai bayyana cewa kasancewarsa tare da Musulmai yayin bukukuwan addininsu na daga cikin ƙoƙarinsa na ƙarfafa fahimtar junansu tsakanin addinai.
Ya bayyana cewa yana halartar bukukuwan Maulidi fiye da 30 a kowace shekara a jihohi daban-daban na Najeriya da ƙasashe maƙwabta.
“A kowace shekara, ina shiga cikin bukukuwan Maulidi fiye da 30 daga wannan jiha zuwa waccan da kuma wasu ƙasashe maƙwabta, da nufin yin biki tare da Musulmai da kuma inganta zaman lafiya, haɗin kai da haƙurin addini,” in ji shi.
Ya yi kira ga Kiristoci da Musulmai da su yi amfani da lokacin Eid-el-Maulud don haɓaka ƙauna, gafarar juna, haɗin kai, da zaman tare cikin lumana a faɗin ƙasar.Fasto Buru ya sami rakiyar Fasto George John, Reverend Rawland Sanda, Gabriel Stephen da sauran mambobin cocinsa zuwa bikin.
Shi ma da yake jawabi, Reverend Rawland Sanda ya ce shugabannin Kirista sun ci gaba da karɓar gayyata daga Musulmai don shiga cikin bukukuwan Maulidi a matsayin ɓangare na ƙoƙarin ƙarfafa dangantaka tsakanin mabiya manyan addinan biyu da nufin samar da ingantacciyar fahimta ga gina zaman lafiya da haƙurin addini.
Ya ce, “A kowace shekara, Musulmai suna gayyatar mu don shiga cikin tarukan Maulidinsu na shekara-shekara, kuma koyaushe muna zuwa don yin biki tare da su saboda mun yi amana da inganta zaman lafiya, haɗin kai da kyakkyawar dangantaka tsakanin mutane na addinai daban-daban.”Sanda ya ƙara da cewa Kiristoci ma suna gayyatar Musulmai zuwa cocinsu lokacin bukukuwan Kirsimeti don tunawa da haihuwar Yesu Almasihu.
“Muna taya Musulmai daukacin faɗin duniya murna kuma muna addu’ar samun zaman lafiya da haɗin kai a ƙasarmu mai daraja,” in ji shi.
Wani malamin Musulunci, Imam Mohammed Musa, da Imam Iliyasu Yusuf Zaria Kaduna sun yaba wa shugabannin Kiristan da suka haɗu da Musulmai don bikin Maulidi, suna masu bayyana al’adar a matsayin abin koyi mai daraja wanda ke haɓaka fahimtar juna da zaman tare cikin lumana.
Sun ce shigar shugabannin Kirista a bikin Maulidi na shekara-shekara ya zama wani muhimmin dandamali na kawo mutane na addinai daban-daban wuri guda da ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai a Jihar Kaduna da Najeriya baki ɗaya.
Sun ce, “Shedun shekaru 11, muna gudanar da bikin haihuwar fiyayyen halitta tare da Fasto Dokta Yohanna Buru a bukukuwan Maulidi daban-daban a Kaduna da wasu sassan arewacin Najeriya.
“Sun yi kira ga gwamnatin tarayya da ta ba shi lambar yabo ta ƙasa saboda inganta zaman lafiya a aikace da kuma haƙurin addini a zahiri.