’Yansandan Delhi sun kai wa wasu Musulmai ’yanjarida hari, bayan sun yi ƙoƙarin yi wa Babbar Ministar Delhi, Rekha Gupta, tambayoyi.
Lamarin dai ya faru ne a yankin Saket na Delhi inda jami’an ‘yansandan na Saket suka shigar da ‘yanjaridar cikin caji office sannan sukayi musu duka.
Lamarin dai ya faru ne a lokacin da yan jarida ciki har da Shaheen Khan da Nafisa waɗanda ke aiki da 4 PM News Network suka je Saket domin ɗaukar rahoton wani taro da Shugabar Gwamnatin Delhi, Rekha Gupta, da Ministan Harkokin Cikin Gida na Tarayyar Indiya, Amit Shah, suka halarta.
Mijin Shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan ya rasu
A yayin taron, Shaheen ta tambayi dalilin da ya sa zaɓaɓɓun jami’an gwamnati ke bai wa wani asibiti mai zaman kansa muhimmanci, alhali batutuwan tsaron mata da matsalar tsaro da oda a birnin na ci gaba da zama abin damuwa.
Wannan tambaya ta haifar da hayaniya, inda ake zargin jami’an ’yan sandan mata da ke wurin sun fitar da ’yan jaridar daga wajen taron da ƙarfi, sannan suka kai su ofishin ’yan sanda da ke kusa. A cewar ’yan jaridar, a nan ne aka ci gaba da dukansu tare da cin zarafinsu.
’Yan jaridar sun kuma yi zargin cewa cin zarafin da aka yi musu ya ƙara tsananta ne bayan jami’an ’yan sandan matan sun gano cewa su Musulmai ne.
A cikin wani faifaian bidiyo da Shafin TRT Africa hausa ta walafa anga ‘yar jaridar mai suna Shaheen tana cewa “Bayan cin zarafina da dukana, sai suka tambayeni sunana. Na gaya musu sunana Khan. Akwai Khan a cikin sunana. Akwai Muhammad a sunana, nu musulma ce, shi yasa ma ayau kai jami’in dansandan a Delhi ka dokeni da kulki, kun mare mu.
Dole ne dole ne. za a dauki mataki. Ba zamu bar maganar a nan ba.
Kiyayyar da aka nuna mana a yau don kawai mu Musulmai ne. Dole ‘yansandan Delhi su yi bayanin hakan. Zaku girbi abin da kuka shuka. Wannan ne hukucin yi wa ministen cikin gida wadannan tambayoyi. ‘yansandan Delhi sun huce haushinsu a kanmu, sun nuna kiyayyarsu.
Kazalika ‘yar jaridar ta nuna yadda ‘yansandan suka lakada wa sauran abokanan aikinta duka da yasa ba zasu iya yin tafiya ba
“Inason na nuna muku abokiyar aikina, yadda suka mata duka da kulki. Kalli waddan n tabban, zan nuna muku na hannuna ma. Kalli hannuna. Kalli yadda akaji min ciwo.
Ita ma daya daga cikin ‘yan jaridar da ta halarci wurin ta bayyana cewa “Ba dukanmu kawai yansandan Delhi suka yi ba a yau, sun doke mu ne bayan sun tambayi addininmu. Ku Musulmai ne?
Bayan sun gane hakan, sai suka doke mu sosai, sannan suka yi mana barazana da cin zarafinmu.
Suka ce idan mu musulmai ne, za su doke mu sau hudu ko ma fiye da haka”.
Sai dai rundunar ’yan sandan Delhi ta musanta zargin cewa jami’anta sun ci zarafin ’yan jaridar.
Rundunar ta ce an cire su daga wajen taron ne saboda wata gardama da ta shafi ajiye mota ba bisa ƙa’ida ba, sannan aka kai su ofishin ’yan sanda domin yi musu tambayoyi.
Zargin da ’yan jaridar suka yi ya zo ne a daidai lokacin da ake ƙara sukar matakin da ’yan sanda suka ɗauka a shafukan sada zumunta, musamman dangane da yadda aka gudanar da ayyukan jami’an tsaro a lokacin zanga-zangar da ta shafi zargin tambayoyin jarabawar NEET a Jantar Mantar da ke Delhi.
Lamarin ya haifar da fushin jama’a da zanga-zanga daga ɗalibai da masu fafutuka a sassan ƙasar.
Matasa masu zanga-zangar na neman a gudanar da bincike mai zaman kansa tare da tabbatar da cewa an ɗora wa waɗanda suka aikata laifin alhaki.
A ranar 3 ga Satumba, ’yar majalisar wakilan jam’iyyar Trinamool Congress (TMC), Mahua Moitra, ta yi kakkausar suka ga ’yan sandan Delhi a wani saƙo da ta wallafa.
0Ta zargi jami’an da cin zarafi da dukan ’yan jaridar biyu a lokacin da suke tambayar gwamnati kan wasu abubuwan da ta kira rashin dacewa, tana mai cewa bai kamata waɗanda suka aikata hakan su tsere wa hukunci ba.
Ana yawan samun rahotannin da ke zargin cewa ’yan jarida Musulmai a Indiya na fuskantar matakan hukuma da ake ganin sun fi shafar su, da suka haɗa da tsarewa, shari’o’i da tsoratarwa ta hanyar amfani da ƙarfi.
Mohammed Zubair, wanda ya kafa shafin binciken gaskiya na Alt News, ya taɓa fuskantar kamu daga ’yan sandan Delhi kan wani saƙon da ya wallafa a kafar sada zumunta a shekarar 2018. Ayyukansa sun haɗa da fallasa kalaman ƙiyayya da ƙungiyoyin masu kishin addinin Hindu ke yaɗawa. Ƙungiyoyin kare ’yancin aikin jarida na duniya sun yi Allah-wadai da kamen, suna kallonsa a matsayin yunƙurin hukunta shi saboda aikinsa na binciken gaskiya.
Haka kuma, ’yan sandan Uttar Pradesh sun kama Siddique Kappan, ɗan jarida da ke aiki da wasu kafafen yaɗa labarai na harshen Malayalam, an kama shi a ƙarƙashin tsauraran dokokin yaƙi da ta’addanci da kuma dokar tayar da zaune tsaye, a lokacin da yake tafiya domin ɗaukar rahoton shari’ar fyade da kisan wata mata a Hathras. Ya shafe sama da shekaru biyu a tsare kafin a ba shi beli.
’Yan jarida biyu daga Kashmir, Asif Sultan da Sajad Gul, su ma sun sha fuskantar tuhume-tuhume a ƙarƙashin tsauraran dokoki, ciki har da UAPA da PSA, sakamakon rahotanninsu ko wasu saƙonnin da suka wallafa a kafafen sada zumunta dangane da ayyukan tsaro a Jammu da Kashmir.
An kuma samu rahotannin cewa ’yan jaridan da ke ɗaukar rahotannin wasu taruka da ƙungiyoyin masu kishin addinin Hindu ke shirya wa na fuskantar warewa, cin zarafi da tilasta musu bayyana addininsu.
Editan hotuna na mujallar Caravan, Shahid Tantray, ya taɓa fuskantar duka daga wasu ’yan Hindu a lokacin da yake ɗaukar rahoto kan rikicin ƙabilanci da addini da ya faru a Delhi a shekarar 2020.
An ce maharan sun nemi katin shaidar sa sannan sukai masa duka bayan sun gano addininsa.
Wasu ’yan jarida mata Musulmai da ke sukar manufofin gwamnati su ma sun fuskanci hare-haren intanet, inda aka wallafa hotunansu da bayanansu na sirri ba tare da izininsu ba a wasu manhajojin bogi na “gwanjon mata”, da aka ƙirƙira domin wulakanta su da kuma tsoratar da su.
Fitattun ’yan jarida mata Musulmai, ciki har da Rana Ayyub da Arfa Khanum Sherwani, sun sha fuskantar hare-haren da ake zargin an shirya su a kafafen sada zumunta, waɗanda suka haɗa da cin mutunci, hotunan bogi na deepfake, fallasa bayanan sirri da kuma barazanar kisa.
Matsin Lamba Kan ’Yan Jarida a Indiya
Masu sukar gwamnati na cewa babban ɓangare na kafafen yaɗa labarai na Indiya ya karkata zuwa ga jam’iyyar Bharatiya Janata Party (BJP) da ƙungiyoyin masu kishin akidar Hindutva.
A irin wannan yanayi, aikin jarida mai zaman kansa ya zama aiki mai haɗari.
A cewar wani rahoto na ƙasa da ƙasa, kusan kashi 3 cikin 100 ne kawai na ’yan jarida a dakunan labarai na Indiya Musulmai. Rahoton ya kuma yi nazari kan rabon ma’aikatan dakunan labarai bisa la’akari da kabila da addini.
A wani babban mataki, ’yan jarida a Indiya na fuskantar matsin lamba daga hukumomi ta hanyar kama mutane ba bisa ƙa’ida ba, takaita ayyukan kafafen sada zumunta, hare-haren jiki da kuma amfani da tsauraran dokoki wajen gurfanar da su a gaban kotu.
Ana zargin amfani da Sashe na 152 na Bharatiya Nyaya Sanhita (BNS) wajen gurfanar da wasu editoci masu zaman kansu da masu sukar gwamnati.
Haka kuma, ana zargin gwamnati da amfani da Dokar Fasahar Sadarwa (IT Act) wajen tilasta wa wasu kamfanonin fasaha takaita ko cire rahotannin labarai da saƙonnin kafafen sada zumunta da ke sukar gwamnati.
’Yan jarida sukan fuskanci tashin hankali da duka daga jami’an ’yan sanda yayin da suke ɗaukar rahotannin zanga-zanga ko wasu tarukan jama’a.
Ƙungiyoyi masu zaman kansu kamar Press Club of India (PCI) na yawan yin Allah-wadai da irin waɗannan hare-hare tare da neman a ɗauki matakin gaggawa kan jami’anda ake zargi da cin zarafin ’yan jarida.
Indiya ta koma baya da matsayi na shida, inda ta kasance ta 157 cikin ƙasashe 180 a cikin World Press Freedom Index na shekarar 2026.
Ƙungiyar Reporters Without Borders (RSF) ta yi nuni da ƙara samun matsin lamba na shari’a kan ’yan jarida, tsangwamar kotu da kuma ƙara amfani da dokokin tsaron ƙasa wajen takaita ayyukan ’yan jarida.
Wannan ya zama abin kunya ga ƙasa, kasancewar ’yancin aikin jarida a Indiya ya kai matakin da ya fi muni a cikin shekaru 25 da aka kwashe ana gudanar da wannan ma’auni na ’yancin aikin jarida.