Tsohon ɗan wasan Ivory Coast, Yaya Touré, ya kafa sabon tarihi bayan ya zama ɗan Afirka na farko da ya jagoranci wata ƙungiya zuwa matakin gasar zakarun Turai ta UEFA Champions League a matsayin babban koci.

Touré ya cimma hakan ne tare da zakarun Slovakia, Slovan Bratislava, bayan da ƙungiyar ta doke NK Celje ta Slovenia da ci 2-1 bayan karin lokaci, inda ta samu nasarar tsallakewa da ci 3-2 jumulla.

Touré, mai shekaru 43, wanda aka nada kocin Slovan Bratislava a watan Yuni, ya jagoranci ƙungiyar ta tsallake zagaye uku na neman gurbin shiga gasar, duk da cewa wannan shi ne karon farko da yake jagorantar ƙungiya a matsayin babban koci.

Nasarar ta zarce abin da ɗan Najeriya Ndubuisi Egbo ya samu a shekarar 2020, lokacin da ya jagoranci KF Tirana ta Albania a wasannin neman gurbin Champions League, amma ƙungiyar ba ta kai matakin gasar ta ƙarshe ba.

Yanzu Touré zai sake komawa gasar Champions League, amma wannan karon a matsayin koci, inda Slovan Bratislava za ta fuskanci Paris Saint-Germain.

Touré ya lashe kofin Champions League a 2009 a matsayin ɗan wasa tare da Barcelona, kuma yanzu zai nemi kafa wani sabon tarihi daga kujerar koci.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *