Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa, FRSC, ta ƙaddamar da wani sabon yunƙuri na ƙasa baki ɗaya domin kawo ƙarshen lodin fiye da kima, da kuma inganta amfani da hanyoyin mota a Najeriya.

An ƙaddamar da yunƙurin ne a Abuja, yayin wani taron wayar da kai mai taken “Ending Overloading, Saving Lives: A National Commitment to Safer Roads and Responsible Transportation in Nigeria.”

Taron ya haɗa hukumomin gwamnati da masu harkar sufuri da masu kaya, hukumomin sa ido, ƙungiyoyin farar hula da kafafen yaɗa labarai.

Shugaban Hukumar kiyaye Haɗurra ta Ƙasa, Shehu Mohammed, ya ce lodin kaya fiye da kima ba laifin da ya sabawa dokokin hanya kadai ba ne, laifi ne wasa da rayuwar al’umma dake amfani da hanyoyi, wanda ke haifar da lalacewar ababen hawa da ci gaban tattalin arziki.

Ya ce, lodin wuce kima na rage ingancin abin hawa, sannan ya yi gargadin cewa haɗa fasinjoji da kaya waje daya kan haifar da mummunar barazana, a duk lokacin da wata matsala ta faru.

A cewarsa, babu wata riba ko rage kuɗin sufuri da ya kai darajar rayuwar ɗan Adam, a saboda haka dole ne masu abin hawa da fasinjoji, hukumomin dake sa ido da gwamnati su ɗauki nauyin tabbatar da tsaron rayukan matafiya.

FRSC, ta ce za ta ƙara ƙarfafa bincike da hukunta masu karya ƙa’ida da wayar da kan jama’a da amfani da bayanan sirri, tare da mayar da hankali kan agajin gaggawa bayan afkuwar haɗari zuwa matakan rigakafi.

Hukumar ta kuma ce bai kamata taron, ya tsaya kan rattaba hannu ba, sai dai ya zama yarjejeniyar aiki tare da kuma nauyi da wa’adin aiwatarwa da tsarin bibiyar sakamako.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *