Wata kotun sasanta rikicin kasuwanci ta ƙasa da ƙasa ƙarƙashin Ƙungiyar Kasuwanci ta Duniya, ICC, da ke birnin Paris, ta yanke hukunci a kan ƙarar da kamfanin Sunrise Power and Transmission Company ya shigar kan gwamnatin Najeriya.

Kotun ta yanke hukunci a ranar 17 ga Satumba, 2026, inda ta yi watsi da buƙatar kamfanin na neman dala miliyan 680 a matsayin kuɗin sulhu da ruwa, dangane da wani rikici da ya shafi aikin samar da wutar lantarki na Mambila mai ƙarfin megawatt 3,960 a Jihar Taraba.

Kamfanin na kuma neman sama da dala biliyan 2.7 a wani sashe na shari’ar, kan diyya da ruwa da suka shafi ci gaban aikin.

Fadar Shugaban Ƙasa ta ce hukuncin ya kawar da wani babban ƙalubalen shari’a da ya shafe shekaru yana kawo cikas ga aikin tashar samar da wutar lantarkin Mambila.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yaba da aikin Ministan Shari’a kuma Antoni Janar na Tarayya, Prince Lateef Fagbemi, da tawagar Ma’aikatar Shari’a wajen kare muradun Najeriya a shari’ar.

Shugaban ya kuma yaba wa tsoffin shugabannin ƙasa Olusegun Obasanjo da marigayi Muhammadu Buhari, wadanda suka bayar da shaida a shari’ar, tare da sauran shaidu da kwararrun da suka taimaka wajen kare matsayin Najeriya.

By Bashar Muhammad Dange

Bashar Muhammad is a Nigerian multimedia journalist, broadcaster, producer, and media professional with years of experience in radio broadcasting, reporting, and content creation. He holds a B.Sc. in Mass Communication from Ahmadu Bello University, Zaria, and a Diploma in Mass Communication from The Polytechnic of Sokoto. Throughout his career, Bashar has produced and presented programmes on current affairs, agriculture, health, education, and community development. He has worked with leading media organizations including Garkuwa FM 95.5 Sokoto, Trimming Radio 96.5 FM Goronyo, Giantability Media Network, and ABU Samaru FM. As a journalist and presenter, he has conducted interviews, reported on social and developmental issues, and amplified the voices of underserved communities. Beyond broadcasting, Bashar has demonstrated leadership in media management, programme development, and team coordination. He has received several awards and recognitions for his contributions to journalism, Hausa language development, and community service. His expertise includes radio production, news reporting, sound editing, investigative journalism, media analysis, and public presentation. Driven by a passion for impactful storytelling and public service, Bashar Muhammad continues to use journalism and media platforms to inform, educate, and empower communities across Nigeria.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *