Karrama Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, ya biyo ƙoƙarin da yake ta fuskar wayar da kan al’umma game da yadda gwamnati ke aikin ta.
Bikin wanda aka shirya a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa a ranar Asabar 27 ga watan Yuni, ya samu wakilcin mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima.
Kyaututtukan da Minista Mohammed Idris ya samu sun haɗar da na kyautata Ƙanana da Matsakaitan Sana’o’i na Ƙasa na shekarar 2026, ƙarkashin tsarin (Renewed hope agenda)
- ’Yan sanda sun kama wasu ’yan’uwa biyu kan zargin yi wa ƙaramar yarinya fyade
- An kama kwamandojin Boko Haram bakwai bayan dawowarsu daga aikin Hajji
Rawar da Ministan ke takawa wajen wayar da kan al’umma game da shirye-shiryen gwamnati na bunƙasa ƙanana da matsakaitan sana’o’i sun kasance abubuwan da akayi la’akari dasu, wajen ƙarfafa masa gwiwar ɗorewa.
Har ila yau gudummuwar sa wajen fito da manufofin gwamnati ta fuskar bunƙasa harkokin kasuwanci da samar da ƙarin guraben ayyukan yi a faɗin ƙasar, na daga cikin abubuwan da masu shirya taron suka zayyano.
A baya bayan Minista Mohammed Idris, ya kasance akan gaba wajen ƙoƙarin wayar da kan al’ummar ƙasa a kafafen yaɗa labarai, game da manifofi da suka shafi gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.